No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Najeriya ta kafa wani kwamiti na musamman don bibiyar yadda farashin iskar gas ta girki ke ci gaba da tashin gwauron zabi a sassan ƙasar.

Wata sanarwar ma’aikatar makamashi ta Najeriyar ta ruwaito minista Ekperikpe Ekpo na bayyana matuƙar damuwa da yadda farashin na gas ke ci gaba da tashi a sassan ƙasar.

A cewar ministan cikin ƙasa da mako guda kwamitin da aka ɗorawa alhakin warware matsalar zai shawo kan tsadar iskar ta gas da kuma aikin rarraba shi zuwa sassan Najeriya.

KU KUMA KARANTA: Amfani da iskar gas na dafa abinci a janareta yana taimakawa masu ƙananan kanfanoni

Rahotanni sun bayyana cewa, farashin gas ɗin na girki ya tashi daga naira 700 kan duk lita guda da ake saye a baya zuwa fiye da naira 900 a yanzu.

A wasu sassa na Najeriyar bayanai sun ce ana sayar da duk lita guda kan farashin fiye da naira dubu 1200.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...