No menu items!

Sample Page Title

Date:

A ranar Laraba ne gwamnatin jihar Katsina ta tabbatar da samun Naira biliyan biyu daga cikin naira biliyan 5 da gwamnatin tarayya ta amince wa jihohi.

Bala Salisu-Zango, kwamishinan yaɗa labarai, al’adu da harkokin cikin gida na jihar ne ya bayyana hakan a lokacin da yake mayar da martani game da jita-jitar cewa gwamnatin tarayya ta saki Naira biliyan biyar ga kowace jiha a faɗin ƙasar.

Ya ce: “An jawo hankalin gwamnatin jihar kan labaran da ke yawo a kafafen yaɗa labarai na cewa gwamnatin tarayya ta saki naira biliyan ga jihohi domin rage raɗaɗi.

“Ina so in bayyana cewa, gwamnatin jihar Katsina ta samu Naira biliyan biyu ne kacal domin sayan hatsi da za a raba wa ‘yan jihar”.

KU KUMA KARANTA: NEMA ta ba da tallafin kayan agaji ga mutane dubu 23 a Nijar

Salisu-Zango ya ce kawo yanzu gwamnatin jihar ta yi amfani da Naira biliyan biyu wajen sayo buhunan shinkafa dubu 40 domin rabawa masu ƙaramin karfi a ɗaukacin rumfunan zaɓe a faɗin jihar.

Ya ce gwamnati za ta kuma yi amfani da kaso na gaba na asusun daga gwamnatin tarayya wajen sayan masara domin rabawa ga magidanta da suka cancanta.

Ya yi gargaɗin cewa gwamnatin jihar za ta ladabtar da duk wanda aka samu yana so a aikin raba kayan agajin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...