No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da kafa kotunan tafi da gidanka domin tabbatar da hukunta masu satar waya a jihar Kano cikin gaggawa.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Dawakin-Tofa ya fitar, ta ce kotunan tafi da gidanka za su yi aiki tare da rundunar haɗin gwiwa ta musamman domin hukunta waɗanda ake tuhuma.

Gwamna Abba ya ce manyan titunan birnin sun haska ne bayan shafe shekaru takwas na duhu yayin da aka kashe fitulun.

“Mayar da fitilun kan titi na cikin ƙoƙarin da sabuwar gwamnati ke yi na magance matsalar fashi da makami da sace-sacen waya da sauran miyagun ayyuka, musamman a babban birnin Kano.”

KU KUMA KARANTA: Gwamnan Kano ya naɗa Akanta-Janar da shugabannin hukumomi huɗu

Aikin da ake ci gaba da gudanarwa ya fara tun ranar Talata kuma zai ci gaba har sai an kuɓutar da kowane ɓangare na jihar daga duhun da ke ba da mafaka ga masu aikata laifuka da ‘yan bangar siyasa,” in ji shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...