No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da kashe Boderi Isyaku ƙasurgumin dan-fashin dajin nan da ya addabi jihohin Kaduna, Katsina, Zamfara Neja da Abuja, tare da wasu manyan ‘yan-bindigan da ke tare da shi.

Gwamnatin jahar Kaduna ta tabbatar da cewa Boderi Isyaku ne da ya jagoranci manyan hare-hare a jihar Kaduna da ma wasu maƙwabtan jahohi, inji muƙaddashin kwamishinan tsaro na jahar Kaduna, malam Samuel Aruwan.

Masana harkokin tsaro irin su manjo Yahaya shinko mai-ritaya na ganin dole a jinjinawa jami’an tsaro kan wannan ƙoƙari amma ya ce wajibi su ci gaba ta tashi tsaye.

KU KUMA KARANTA:Za’a buɗe sabuwar ma’aikatar wutar lantarki a jihar Abiya

A hirar shi da Muryar Amurka, Alh. Ɗayyabu Kerawa wanda ya jagoranci al’ummar garuruwan da ke yammacin Zariya da su ka yi koke a kan yadda ‘yan-bindiga ke kai hare-hare a yankunan su, kuma ya ce jin labarin kashe ƙasurgumin ɗan-fashin dajin ya sa sun fara ji akwai yuwuwar su koma noma bana.

Cikin watan Fabarairun nan dai ‘yan-bindiga sun kai hare-hare a wasu yankunan ƙananan hukumomin Igabi, Giwa, Chukun, Ƙaura da Kajuru sai dai ana sa ran wannan nasarar kashe ‘yan-fashin dajin, ka iya kawo ƙarshen barazanar tsaro a waɗannan yankuna.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...