No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa ta nuna damuwarta kan ƙarancin sabbin takardun kuɗi na Naira, inda ta ce mazauna jihar na kwana a wajen injin bada kuɗi.

Kwamishinan kuɗi da ci gaban tattalin arziki na jihar, Babangida Gantsa, ya ce a ziyarar da ya kai wasu bankunan kasuwanci a jihar a ranar Larabar da ta gabata, kwastomomi akalla 250 ne suka yi layi a na’urar cire kuɗi ta ATM.

Gantsa ya bayyana cewa rashin samun takardar kuɗi na Naira a wurare dabam-dabam ya gurgunta harkokin tattalin arziki da sauran rayuwar al’umma a Jigawa.

KU KUMA KARANTA:CBN zai hukunta duk bankunan da ke ɓoye sabbin kuɗi

“Za ka iya gani da kanka, mutane suna kwana a ATMs suna yin layi suna cire kudi daga bankunan kasuwanci. “Abin da ya damu da lamarin, sai (Mai girma Gwamna) ya bukaci in zagaya bankunan kasuwanci a babban birnin ƙasar inda shugabannin bankunan suka tabbatar min da cewa babban bankin Najeriya ya hana su isassun kuɗaɗe da za su yi lodi a ATM don mutane su cire.

“Akwai wurin ATM guda ɗaya da na kirga mutane 215 da ke jiran cire kuɗi. A wasu bankuna, ATM yana da fiye da 250 a cikin ATM guda ɗaya.

Sun ce da yawa daga cikinsu suna kwana a can. “Matsalolin sun riga sun gurgunta harkokin kasuwanci a jihar sakamakon rashin sabon takardar Naira.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...