Connect with us

Labarai

Gwamnan Yobe ya yaba wa jami’an tsaro wajen ƙoƙarin dawo da zaman lafiya a jihar

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Mai Girma Gwamnan Jihar Yobe Alhaji Mai Mala Buni CON (Chiroman Gujba) a ranar Asabar 2 ga Satumba 2023, ya karɓi baƙuncin babban hafsan sojin ƙasa, Laftanar Janar TA Lagbaja wanda ya kai wa Gwamnan ziyara a gidan gwamnati da ke birnin Damaturu.

Da yake maraba da babban hafsan hafsoshin sojan ƙasan, Gwamna Buni ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da neman goyon baya da haɗin kan sojojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro a kowane lokaci.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Yobe ta raba kayan abinci a Potiskum, don rage raɗaɗin rayuwa

A wata takarda da sakataren yaɗa labaran mataimakin gwamnan jihar Yobe, Hussaini Mai Sule ya fitar, ya ce, Gwamnan ya samu wakilcin mataimakinsa Alhaji Idi Barde Gubana (Wazirin Fune) ya godewa hafsan sojojin bisa wannan ziyarar tare da nuna jin daɗinsa da ƙoƙarin jami’an tsaro na yaƙi da ta’addanci da sauran laifuka a jihar. Ya yi nuni da cewa sojoji sun yi ƙoƙari sosai wajen dawo da zaman lafiya a jihar Yobe da sauran sassan yankin Arewa maso Gabas.

Ya kuma yi ƙira ga jami’an tsaro da su haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen ganin sun dawo da cikakken zaman lafiya domin jama’a su yi aiki a gonakinsu ba tare da wata fargaba ba.

Tun da farko da yake jawabi yayin ziyarar, babban hafsan sojin ƙasa, Laftanar Janar TA Lagbaja, ya bayyana cewa ya je jihar ne domin rangadin rundunonin soji da runduna a yankin Arewa maso Gabas.

Ya ce a matsayinsa na babban hafsan soji yana sane da ƙalubalen da ake fuskanta a kewayen Damasak da Gaidam da sauran wuraren da ‘yan ta’adda ke ci gaba da yin barazana. Babban hafsan sojojin ya jaddada cewa yana ƙoƙarin shawo kan matsalar cikin gaggawa.

Lagbaja ya yabawa gwamnati da al’ummar jihar Yobe bisa gagarumin goyon bayan da aka baiwa sojojin Najeriya.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Gwamnatin Zamfara ta zuba jami’an tsaro a wasu muhimman wurare a jihar | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like