No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Gwamnan Jihar Yobe Alhaji Mai Mala Buni CON, ya je Katsina yau domin yin ta’aziyya ga Alhaji Ɗahiru Barau Mangal, bisa rasuwar matarsa, Hajiya Aisha Mangal, wadda ta rasu a ƙarshen makon da ya gabata.

Gwamnan ya bayyana rasuwar marigayiyar Hajiya A’isha a matsayin babban rashi, uwa kuma mai taimakon jama’a da ‘yan uwa da jihar Katsina da sauran al’umma za su yi kewarta.

‘Ina roƙon Allah (T) ya gafarta mata kura-kuranta, ya kuma sa ta huta, ya sa Aljannatul Firdausi.

“Hakazalika ina addu’ar Allah ya jajantawa iyalan Barau Mangal, ya kuma basu ikon jure wannan babban rashi” Gwamna Buni ya yi addu’a.

Alhaji Ɗahiru Barau Mangal, hamshaƙin attajirin nan na Katsina, ya kasance yana da alaƙa da gwamnatin Buni da ci gaban jihar Yobe.

KU KUMA KARANTA: Buhari, Tinubu sun miƙa ta’aziyyar rasuwar matar Aminu Ɗantata

Ya bayar da gudumawa sosai a wajen ƙaddamar da asusun neman ilimi na jihar Yobe domin tallafawa ci gaban ilimi a jihar Yobe.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...