Connect with us

Labarai

Gwamnan Neja ya ba da hutun kwana uku, don raba kayan rage raɗaɗi

Published

on

Gwamnan jihar Neja, Umaru Baƙo, ya ayyana kwanaki uku na hutun jama’a domin ba da damar rabon kayan agajin gaggawa na naira biliyan 5.23 ga mazauna ƙananan hukumomi 25 na jihar.

Yayin da yake fitar da hanyoyin raba kayayyakin, gwamnan ya yi gargaɗin cewa duk wanda ya kawo cikas a wajen raba kayan agajin zai iya fuskantar ɗauri a gidan yari.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da manema labarai a gidan gwamnati da ke Minna ranar Juma’a.

Ya ce za a fara hutun ne daga ranar Laraba 6 ga Satumba zuwa Juma’a 8 ga Satumba.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Yobe ta raba kayan abinci a Potiskum, don rage raɗaɗin rayuwa

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta karɓi Naira biliyan biyu da manyan tireloli na shinkafa daga gwamnatin tarayya, inda ya ƙara da cewa har yanzu gwamnati na sa ran za ta biya bashin naira biliyan 2 da buhunan masara 40,000 daga gwamnatin tarayya.

Ya ƙara da cewa, saboda gwamnatin jihar ba za ta iya jira gwamnatin tarayya ta aika a daidai lokacin da jama’a ke shan wahala ba, hakan ya sa gwamnatin jihar ta yanke shawarar ƙara tallafin domin ta kai ga gaci.

Gwamna Bago ya yi nuni da cewa, dukkan jami’an gwamnati, ma’aikatan gwamnati, masu riƙe da muƙaman siyasa, jam’iyyun siyasa, da ’yan ƙwadago za su shiga aikin raba kayan jin daɗin jama’a, wanda zai kasance a matakin zaɓe da kuma unguwanni.

Ya ƙara da cewa kwanaki uku na hutun jama’a ne domin tabbatar da cewa duk masu riƙe da muƙaman siyasa da masu riƙe da muƙaman gwamnati sun koma ƙananan hukumomi da unguwanni don kula da yadda za a raba kayan tallafin.

Ya ce: “Za a raba Naira miliyan 10 ga kowace shiyya a ƙananan hukumomi 21 yayin da ƙananan hukumomin Bida, Suleja, Kontagora, da Chachanga za su samu Naira miliyan 20 kowace.

Naira miliyan 80 za a tafi da su cibiyoyin gargajiya don ka da su sa hannu a kan abin da ake nufi da jama’a, za a ba wa ‘yan gudun hijira Naira miliyan 75, a baiwa jam’iyyun siyasa Naira miliyan 150 don ka da a karkatar da kayan agaji, da Naira miliyan 110 na kayan aiki da tsaro.

“Gwamnatin tarayya tana aiko mana da buhunan masara 40,000, muna da rumfunan zaɓe 4,950, muna raba buhun masara guda 10 a kowace rumfar zaɓe. Za mu ƙara ƙarin buhu 10,000 wanda zai kashe mu Naira miliyan 575.

Jimlar darajar za ta zama N5, 230,550,000. Jihar za ta ƙara Naira biliyan 230 zuwa Naira biliyan 5 da gwamnatin tarayya za ta bayar.

“Za a dagula kuɗaɗen a ranar Litinin zuwa asusun ƙananan hukumomin. Dole ne kowa ya je ya zauna a unguwanni da ƙaramar hukumarsa.

Kada ku sayi shinkafa. Idan mutanenka sun saba cin wake ko dawa, ka saya musu.

Ƙaramar hukuma da gundumomi za su yanke shawarar abin da za su saya. Mun yanke shawarar cewa ba za mu karkasa wannan kuɗi ba domin mu mayar da dukiyar ga jama’a,” inji shi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like