No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnan Neja, shugaban kiristoci sun yi Alla-wadai da bankawa coci wuta

Daga Ali Sanni Larabawa

An banka wa cocin na Christian Church of God wuta a kan titin Kwalejin Ilimi mai zurfi ta tarayya da ke Kontagora a ranar Asabar, kuma akayi wawason kayan ciki.

Gwamna Umar Bago na jihar Neja, ya fusata tare da yin kakkausar suka ga waɗanda suka banka wa Cocin Redeemed wuta a Kontagora .

Gwamna Bago yace wannan ɓarna rashin hankali ne da rashin mutunci.

An ruwaito cewa an taɓa banka wa cocin wuta shekaru 10 da suka wuce, bayan wasu ɓata garin yara sun yi barazanar rashin amincewa a ƙarasa ginin cocin.

KU KUMA KARANTA: Aƙalla mutum 20 sun mutu a Bayelsa bayan da kwale-kwalensu ya kama da wuta

Shugaban ƙungiyar Kiristocin jihar Neja, Bulus Yohanna ya yi tir da wannan barnar.

Yohanna ce dabbanci ne kuma bai kamata ba. Kuma ya yi ƙira ga gwamnati ta ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki tare da kamo waɗanda suka yi wannan aika-aikar. “Tunda akwai dokar ‘yancin kowa ya yi addininsa a faɗin Najeriya.

Cocin dai kamar yadda Mataimakin Faston, Samson Ogbebor ya bayyana takai kimanin shekaru 20 da ginawa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...