Gwamnan Katsina Dikko Raɗɗa, ya naɗa sakataren gwamnati da wasu da dama

Gwamnan jihar Katsina Umar Dikko Raɗɗa ya naɗa Ahmed Dangiwa a matsayin sakataren gwamnatin jihar.

A wata sanarwa da shi da kansa ya sanya wa hannu a ranar Litinin, gwamnan ya kuma naɗa Jabiru Tsauri a matsayin shugaban ma’aikatan jihar da Mukhtar Saulawa a matsayin mataimakin shugaban ma’aikatan, sai Abdullahi Turaji a matsayin babban Sakataren Gwamnan.

Sauran naɗin da Gwamna Raɗɗa ya amince da su sun haɗa da Maiwada Danmallam a matsayin babban Darakta na yaɗa labarai, Ibrahim Kaula Mohammed a matsayin babban sakataren yaɗa labarai, Miqdad Isah a matsayin babban mataimaki na musamman (Digital Media) da Abubakar Jikamshi a matsayin Babban Mataimaki na Musamman (Print and Electronic Media).

KU KUMA KARANTA: Sabon Gwamnan Kano Abba Gida-Gida, ya naɗa shugaban ma’aikata da sakataren gwamnati

Gwamnan ya kuma naɗa Bishir Maikano a matsayin babban mataimaki na musamman (Protocol) na Gwamnan.

Sauran naɗin sun haɗa da Hassan Danhaire a matsayin babban mataimaki na musamman (Special Services) mataimakin gwamna da Ahmed Rabiu a matsayin mai ɗaukar hoto na gwamna.

Gwamnan ya taya sabbin waɗanda aka naɗa murna tare da buƙace su da su haɗa kai da shi wajen ganin an dawo da dukiyar jihar.


Comments

2 responses to “Gwamnan Katsina Dikko Raɗɗa, ya naɗa sakataren gwamnati da wasu da dama”

  1. […] KU KUMA KARANTA: Gwamnan Katsina Dikko Raɗɗa, ya naɗa sakataren gwamnati da wasu da dama […]

  2. […] KU KUMA KARANTA: Gwamnan Katsina Dikko Raɗɗa, ya naɗa sakataren gwamnati da wasu da dama […]

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *