Connect with us

Labarai

Gwamnan Kano ya bayyana kyautar N35,000 ga ma’aikata da ‘yan fansho a jihar

Published

on

Gwamna Abba Kabir Yusuf ta sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da ƙungiyar kwadago ta Najeriya NLC da TUC domin bayar da kyautar N35,000 ga ma’aikata da ‘yan fansho a jihar.

Yarjejeniyar na nufin rage matsalolin tattalin arziki da ma’aikatan gwamnati ke fuskanta a jihar Kano bayan cire tallafin man fetur.

Comrade Mubarak Buba Yarima, shugaban ƙungiyar TUC reshen Kano ne ya tabbatar da hakan a ranar Talata, inda ya jaddada muhimmiyar rawar da ƙungiyoyin ƙwadago ke takawa wajen tattaunawa da gwamnati.

Yarjejeniyar ta samo asali ne biyo bayan roƙon haɗin gwiwa da NLC da TUC suka gabatar wa gwamnatin jihar Kano a watan Oktoban 2023, suna neman a shiga tsakani a cikin matsalolin tattalin arziki da ake fama da su.

A martanin da Gwamna Yusuf ya mayar, nan take ya kafa kwamiti na musamman domin tantance lamarin. Binciken kwamitin ya kai ga cimma matsaya kan cewa za a fara biyan N20,000 daga watan Disamba 2023 ga dukkan ma’aikatan gwamnati a matakin jihohi da ƙananan hukumomi.

KU KUMA KARANTA: Gwamnan Kano ya ƙaddamar da ayyukan gadar gadojin sama a jihar

Yarima ya ƙara da cewa za a ci gaba da bayar da tallafin kuɗi har sai an gudanar da cikakken nazari kan mafi ƙarancin albashi a cikin watanni shida masu zuwa.

Bugu da ƙari, masu karɓar fansho za su riƙa karɓar N15,000 duk wata na tsawon watanni uku, tare da biyan bashin alawus ɗin Disamba 2023 da suka rasa.

Yarima ya bayyana jin daɗinsa ga gwamnatin jihar Kano, musamman ma mai baiwa gwamna shawara kan harkokin ƙwadago, Kwamared Baffa Sani Gaya, da sauran mambobin kwamitin bisa gaggaruwar bincike da miƙa kai ga gwamnan.

Tun da farko dai ƙungiyoyin ƙwadago sun yi barazanar yajin aikin a faɗin ƙasar domin bayyana ƙalubalen da ma’aikata ke fuskanta bayan cire tallafin man fetur da shugaba Bola Tinubu ya yi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

Published

on

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

An jiyo Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Neja yana ba da umarnin jami’an tsaronsa da su yi wa wani malamin addinin Islama cin mutunci a yayin bikin addu’ar Fidda’u ga matar mataimakinsa, Hajiya Zainab Yakubu Garba da ta rasu.

Lamarin wanda ya auku a Minna a ranar Juma’a, ya auku ne a lokacin da malamin ya sadaukar da kansa domin gudanar da addu’a, lamarin da aka ce ya harzuƙa Gwamna Bago.

A cikin faifan bidiyon, ana iya jin Gwamna Bago yana jawabi ga masu jajantawa, inda ya nuna cewa za a iya gudanar da addu’o’i ga marigayiyar a cikin gida, kafin daga bisani ya fusata a lokacin da malamin ya fito.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Ya tuhumi malamin, sannan ya umurci jami’an tsaronsa da su ɗauki mataki, inda ya umarce su da su yi masa mari mai kyau sannan su kama shi.

Shaidu da suka halarci taron sun nuna kaɗuwa dangane da wannan hali na gwamnan, inda suka yi la’akari da irin tsaurin ra’ayinsa ga malamin.

Wannan lamari dai ya ƙara rura wutar zarge-zargen da ke tattare da yadda Gwamna Bago ke da alaƙa da cin zarafi ga mataimaka da magoya bayansa, kamar yadda SaharaReporters ta ruwaito kuma majiyar gwamnan ta tabbatar.

Kalli bidiyon a nan:

Continue Reading

Labarai

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

Published

on

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

Ministocin kuɗi da Gwamnonin manyan Bankunan ƙasashen ƙungiyar raya tattalin arzikin Yammacin Afirka 15, sun ci gaba da shirye-shiryen ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da aka yiwa laƙabi da ECO.

Wannan yunƙuri da ke da nufin haɓaka tattalin arziƙi yankin Afirka ta Yamma, ya samu amincewar tarayyar Najeriya.

A wata sanarwa da ma’aikatar kuɗi ta Najeriyar ta fitar jiya juma’a, ɗauke da sa hannun Daraktan watsa Labarai, Mohammed Manga, ta ce Ministan Kuɗin ƙasar Wale Edun, ya lura da muhimmiyar rawar da kuɗin na bai ɗaya zai taka wajen bunƙasa ci gaban tattalin arziƙi, da kuma ci gaban yankin baki ɗaya.

KU KUMA KARANTA:ECOWAS na buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don kafa rundunar tsaro – Badaru

Edun, ya kuma jaddada ƙudirin Najeriya na ci gaba da shiga gaba wajen aiwatar da shi, wanda ake ganin wani ɓangare ne daga shirin hukumar yin katin ɗan ƙasa na samar da kati guda mai amfani a wurare uku, wanda ake sa ran zai fara aiki a watan Agusta mai zuwa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like