No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya amince da naɗin muƙamai guda 14.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran sa, Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Alhamis a Kano.

A cewar sanarwar, an naɗa Dakta Sani Ɗanjuma a matsayin babban mataimaki na musamman, (SSA), harkokin mulki; Bello Nuhu Bello, SSA na gudanarwa; Najeeb Bashir Nasidi, SSA na harkokin cikin gida; Dakta Abdurraman Kirare, SSA na harkokin cikin gida II da Safwan Garba, SSA ayyuka na musamman.

Sauran su ne Abdulƙadir Balarabe Kankarofi, SSA Protocol I; Salisu Yahaya Hotoro, SSA na kafafen yaɗa labarai na zamani; Mataimaki na Musamman, SA, Salisu Muhammad Kosawa; SA Social Media da Zulaihat Yusuf Aji, SA
mai ba da shawara na musamman kan Kafofin Watsa Labarai.
Rasheedat Usman, SA Secretariat, Personal Assistants, PAs, Ahmad Aminu Yusuf, PA Domestic, Ahmad Muhammad Gandu, PA Videography,  Isa Muhammad Giginyu, PA Photography da  Hassan Kabir, PA Social Media.

Sanarwar ta ce dukkan naɗe-naɗen sun fara aiki nan take.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...