No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum ya sake naɗa Malam Isa Gusau a matsayin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da dabaru.

Haka kuma gwamnan ya naɗa wasu goma sha ɗaya a matsayin manyan mataimaka na musamman da manyan manajoji da sakatariyar zartarwa.

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa Gusau ya yi aiki da mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shattima a lokacin yana gwamnan jihar Borno kafin ya ɗauki irin wannan naɗin da Zulum a zamaninsa na farko.

Haka kuma gwamnan ya sabunta naɗin na Hon. Baba Shiekh Haruna a matsayin babban mataimaki na musamman kan harkokin yaɗa labarai; Hon. Abdul Rahman Ahmed Bundi a matsayin babban mataimaki na musamman kan sabbin kafafen yaɗa labarai.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Zulum ya ba da umarnin a binciki likitocin da suka ƙi karɓar mutanen da suka yi hatsarin mota

Ya kuma naɗa Ambasada Adamu Abbas a matsayin babban manazarci kuma mai bincike; Hon Injiniya Baba Bukar Gujbawu, mai ba da shawara na musamman kan sa ido da tantancewa da Dakta Mairo Mandara a matsayin babbar mai ba da shawara kuma mai gudanarwa, ci gaba mai ɗorewa, haɗin gwiwa da tallafin jin ƙai.

Sauran waɗanda aka naɗa sun haɗa da Hon. Ahmed Sanda – mai ba da shawara na musamman kan yarjejeniya; Injiniya Ibrahim Idris a matsayin mai ba da shawara na musamman, ayyuka na musamman; Hon. Ibrahim Dangana (Relay) – mataimaki na musamman kan Protocol; Hon. Umar Mohammed a matsayin babban manaja, gidan rediyon Borno (BRTV); Dakta Babakura Mamman Gadai a matsayin babban sakataren hukumar raya ci gaba ta jihar Borno, haɗin gwiwa da bayar da agajin jin ƙai, sai kuma Liman Gana Mustapha a matsayin babban manajan hukumar tsara birane da raya birane ta jihar Borno.

Wata sanarwa da Barista ya raba wa manema labarai ranar talata a Maiduguri.

Mustapha Ali Bogusuma, babban sakataren gwamnati ya bayyana cewa Gwamna Zulum ya yi waɗannan naɗe-naɗen ne bisa la’akari da cancanta da kuma bayanan shekarun baya a aikin gwamnati.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...