No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnan Yobe zai ƙaddamar da sabon shirin tallafin noma na bana

A wani yunƙuri na ci gaba da bunƙasa harkar noma da ƙarfafa gwiwar manoma a karkara, Mai Girma Gwamnan Jihar Yobe, Alhaji (Dr.) Mai Mala Buni, CON, zai ƙaddamar da wani sabon Babban Shirin Tallafin Noma domin kakar noman shekarar 2025.

Za a gudanar da wannan muhimmiyar ƙaddamar wa a gobe Talata, 29 ga Yuli, 2025 a filin wasa na August 27 Stadium da ke Damaturu, da misalin ƙarfe 2:00 na rana.

Wannan sabon shiri na bana yana ci gaba ne da matakin da Gwamna Buni ya dauka a bara, inda ya kaddamar da babban shirin tallafin noma mai darajar naira biliyan 14 (₦14bn) domin bunkasa samar da abinci, samar da ayyukan yi da kuma karfafa zaman kace wando ga al’ummar jihar.

KU KUMA KARANTA: Gwamnan Yobe ya zama shugaban ƙungiyar gwamnonin Tafkin Chadi

Shirin bana na 2025 zai kara daukaka wannan tsari, inda za a raba sabbin kayan aikin noma, traktoci, taki, injinan noma na hannu don karfafa noma na zamani a cikin kananan hukumomi 17 na jihar.

Gwamnatin Gwamna Buni na ci gaba da jajircewa wajen inganta noma a matsayin ginshikin tattalin arziki, ci gaban karkara, da rage talauci, musamman a wannan lokaci da kasar ke fuskantar kalubalen rashin wadataccen abinci.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...