No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamna Dauda Lawan na Zamfara ya amince da naira biliyan 4 don gyara hanyoyin cikin Gusau a matakin farko.

Jami’in hulɗa da jama’a na ma’aikatar ayyuka da sufuri, Idris Mainasara ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Gusau ranar Alhamis.

Idris Mainasara mai ba da shawara na musamman kan samar da ababen more rayuwa da raya birane, Ibrahim Agege ya sanar da cewa an bayar da kwangilar ne ga kamfanin Ronchess Global Resources PLC.

KU KUMA KARANTA: Hukumar CSDA ta horar da ma’aikata 886 a Zamfara

Hanyoyin da ake sa ran za a gyara sun haɗa da Bello Barau daura da ofishin ‘yan sanda na Gusau, Bello Barau daura da gidan gwamnati, Bello Barau daura da Tsohuwar Kasuwa, Junction ‘yan Kekuna, fadar sarki da Rankin Ruwa duk a cikin birnin Gusau.

Don haka gwamnatin jihar ta nemi goyon baya da haɗin kan mai martaba Sarkin Gusau Ibrahim Bello domin wayar da kan mutanen da ayyukan ya shafa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...