Connect with us

Ƙasashen Waje

Guinea ta takaita sadarwar intanet saboda matsalar tsaro

Published

on

Ministan harkokin wajen Guinea ya shaida wa jami’an diflomasiyya cewa tsaikon da ake samu a kan intanet a ƙasar na faruwa ne saboda wata matsalar tsaro, a wani jawabin da aka watsa a gidan talabijin na ƙasar.

Kimanin jakadun ƙasashe 15 ko wakilansu ciki har da wakilai daga ƙungiyar Tarayyar Turai da Amurka da China ne suka gana da Morissanda Kouyate domin kokawa kan rashin ingancin intanet, kamar yadda jawabin da aka watsa ranar Laraba da maraice ya nuna.

Sun koka a kan keta ‘yancin faɗar albarkacin baki da rashin samun intanet da rashin man fetur bayan an yi mummunar gobara a babban wurin ajiyar fetur a ƙasar a watan Disamba da kuma matsalolin da ke fuskantar ma’aikatansu.

An kwashe makonni ana fama da matsanancin rashin intanet a Guinea, wadda sojojin da suka yi juyin mulki a shekarar 2021 suke mulka.

KU KUMA KARANTA: Muna ƙoƙarin kakkaɓe matsalar tsaro amma har yanzu ba mu yi nasara ba — Tinubu

Mahukunta kuma sun sanya sharuɗɗa kan kafafen watsa labarai masu zaman kansu yayin da aka katse kafafen sada zumunta da kuma gidajen rediyo masu zaman kansu tare da shafukan intanet na jaridu sannan ake kamawa ko far wa ‘yan jarida.

“Ta shafi dukkanmu, wata matsalar tsaro ta shafe mu,” in ji Kouyate a cikin jawabin da ya yi a talabijin.

Bai ba da ƙarin bayani ba game da matsalar. “Ba za mu iya ƙara bayani a kai ba,” in ji shi.

Ministan na harkokin waje ya kuma shaida wa jami’an diflomasiyya cewa matsalolin da ofisoshin jakadancinsu ke funkanta sun shafi ma’aikatan ƙasar Guinea ma.

“Game da matsalar sadarwa, akwai wannan matsalar a fadar shugaban ƙasa,” a cewarsa, yana mai ƙarawa da cewa za su warware matsalar nan ba da jimawa ba.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta koka a ƙarshen watan da ya gabata game da “ƙaruwar take ‘yancin ‘yan jarida ” a Guinea kuma ta yi ƙira ga hukumomi su sauya yanayin nan-take.

Kanar Mamady Doumbouya, shugaban gwamnatin mulkin soja ta ƙasar, ya yi alƙawarin miƙa mulki ga farar-hula a watan Janairun shekarar 2026.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Published

on

Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar

Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Published

on

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.

Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.

COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.

Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.

Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like