Connect with us

Al'ajabi

Guguwa mai ƙarfi ta kashe mutane 11 a Pakistan

Published

on

Wata mahaukaciyar guguwa mai ƙarfin gaske ta kashe aƙalla mutane 11 daga wata ƙabilar makiyaya ciki har da wani yaro ɗan shekara huɗu suka mutu sakamakon mahaukaciyar guguwa a arewacin Pakistan.

Dusar ƙanƙara ta faɗo a lokacin da ƴan ƙungiyar suka tsallaka wani yanki mai tsaunuka tare da garken awakinsu.

An kuma samu jikkatar wasu mutane 25, inda ake ci gaba da aikin ceto.

Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif ya bayyana alhininsa game da mutuwar mutanen, inda ya ce al’amura irin su ƙanƙara na ƙaruwa saboda sauyin yanayi.

Ruwan sama kamar da bakin ƙwarya ya auku ne da sanyin safiyar ranar Asabar a wani ɓangare na hanyar da ta bi ta gundumar Astore na yankin Gilgit Baltistan zuwa maƙwabciyarta Azad Kashmir, a yankin Kashmir da ke ƙarƙashin Pakistan.

KU KUMA KARANTA: Ruwan sama ya kashe mutane 7, ya raunata da dama a Delta

Wasu mata huɗu da yaro ɗan shekara huɗu na daga cikin waɗanda suka mutu, kamar yadda babban jami’in ‘yan sanda Ziarat Ali, ya faɗa wa kamfanin dillancin labarai na AFP.

Jami’an aikin ceto sun fuskanci ƙalubale saboda nisa da kuma wahalar zuwa da yankin yake da shi.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Hukumar ba da agajin gaggawa ta tarayya ta yi gargaɗin samun iska mai ƙarfi a jihohi 12 | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Guguwar iska ta lalata gonakin kaji, ta kashe tsuntsaye dubu uku a Filato | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: Guguwar Haikui ta mamaye yankin Taiwan, ta jiklata mutane da dama | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like