Connect with us

Gobara

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Published

on

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Gobara ta tashi da yammacin yau a wani sashe na matatar man Ɗangote da ke kusa da Lekki a Legas.

Jami’an agajin gaggawa sun ɗauki matakin shawo kan lamarin, kuma a cewar rahotannin farko, ba a samu raunuka ba.

Kawo yanzu dai ba a san musabbabin tashin gobarar ba, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike don gano girman barnar da aka yi da kuma abin da ya haddasa faruwar lamarin.

Da take mayar da martani kan gobarar a cikin wata sanarwa da Ɗangote ya fitar, mai ɗauke da sa hannun Anthony Chiejina, ƙungiyar ta ce, “Mun yi gaggawar shawo kan wata ‘yar karamar gobara a masana’antar sarrafa iska (ETP), a yau Laraba 26 ga watan Yuni.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta kashe jarirai shida a Indiya

“Babu wani dalili na tashin hankali yayin da matatar ta ke aiki kuma babu wani rauni da aka samu ko lahani ga dukkan ma’aikatanmu da ke bakin aiki.”

Matatar dangote wani katafaren aiki ne da ake ginawa wanda ake hasashen zai iya tace ganga 650,000 a kowace rana.

Boko Haram

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

Published

on

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An kasha aƙalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai a jihar Borno a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.

Borno dai na cikin shekaru 15 na hare-haren masu iƙirarin kishin Islama wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane tare da raba wasu miliyoyi da humallan su.

Duk da cewa sojojin Najeriya sun rage ƙarfin mayaƙan, amma har yanzu suna kai munanan hare-hare kan fararen hula da kuma wuraren tsaro.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Barkindo Saidu, shine babban Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno, ya ce wasu da ake zargin ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai hari daban-daban a wajen bikin aure da jana’iza da kuma asibiti, inda suka kashe mutane tare da jikkata wasu da dama a garin Gwoza.

Saidu ya ce an tabbatar da mutuwar mutum 18, adadin da ya haɗa da ƙananan yara da manya da ma mata masu juna biyu.

Sai dai babu wata ƙungiyar ko wani mutun da ya ɗauki alhakin kai wannan harin.

Boko Haram da ISWAP da ta ɓalle kanta, su ne ƙungiyoyin ‘yan bindiga da suka fi yawan gudanar da ayyukan su a jihar Borno, wani babban yanki na karkara mai girman gaske.

Continue Reading

Gobara

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Published

on

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya miƙa saƙon jajensa ga ‘yan kasuwar da shaguna da dukiyoyinsu suka ƙone a gobarar da ta tashi a kasuwar Karu a daren Alhamis.

Sanarwar da hadimin shugaban ƙasar akan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngilale ya fitar a ranar Juma’a ta ce, shugaban ƙasar ya yi takaicin samun labarin gobarar da ta shafi wani sashe na kasuwar.

Da yammacin ranar Alhamis, gobara ta laƙume wani yanki na kasuwar, inda ta lalata ɗimbim dukiya da sauran kayayyaki masu daraja.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Sanarwar ta ƙara da cewar, shugaban ƙasa na miƙa saƙon jajensa ga ilahirin ‘yan kasuwar da wannan mummunan al’amari ya shafa, sannan yana ba su tabbacin samun tallafi daga gwamnatinsa.

Shugaban ƙasar ya kuma yi ƙira da a riƙa taka tsantsan da ɗaukar matakan kariya, domin kare afkuwar gobara da sauran bala’o’i a nan gaba.

Continue Reading

Gobara

Mutane da dama sun mutu, sakamakon fashewar tankar mai a Fatakwal

Published

on

Ana fargabar mutane da dama sun rasa rayukansu bayan da wata tankar mai ta kama da wuta a hanyar East-West Road a birnin Fatakwal da ke jihar Rivers a kudancin Najeriya.

Jaridun Punch da na Vanguard sun ruwaito cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:45 na daren Juma’a.

Bayanai sun yi nuni da cewa bayan da tankar ta mai ta kama da wuta, ta shafi motoci aƙalla goma da ke jerin cunkoson ababen hawa a birnin na Fatakwal.

KU KUMA KARANTA:Matatar man Fatakwal za ta koma bakin aiki cikin watan Afrilu – Kyari

Wani da ya shaida lamarin ya faɗawa jaridar Vanguard cewa ya ji ƙara har sau biyu masu firgitarwa daga baya kuma hayaƙi ya turnuƙe sararin samaniya.

“Idan kuna da ‘yan’uwa a Fatakwal ku ƙira su don ku ji lafiyarsu” Wani mazaunin birnin na Fatakwal mai suna Bassey Esang Don, ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto ba a san musabbabin fashewar da ta auku ba ko iya sanin adadin mutanen da suka mutu.

Faɗuwar tankar mai ta kama da wuta ba baƙon abu ba ne a Najeriya, inda a wasu lokuta mutane kan yi rububin zuwa kwasar man idan yana Malala.

Daga nan ne kuma akan samu akasi har wuta ta kama ta laƙume rayukan mutane.

Wannan al’amari na faruwa ne yayin da farashin mai ya ƙara tsada a Najeriya inda litar mai ta kusa kai wa Naira 1,000 a sassan ƙasar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like