No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumomi a Nepal sun ce girgizar ƙasa ta kashe mutane aƙalla 130 a Yammacin ƙasar.

An tura jami’an tsaro wurin da lamarin ya faru a yankin Jajarkot, mai nisan kilomita 500 daga Yammacin Kathmandu.

Girgizar ƙasar ta faru ne a tsakar dare, kuma ta fi shafar yankin Jarjarkot wanda bai wuce nisan kilomita 500 ba daga Ktahmandu babban birnin ƙasar.

Mutanen sun riƙa fita daga gidajen su cikin ɗimuwa, kuma hotunan da kafafen yaɗa labaran ƙasar suka fitar sun nuna yadda gidaje suka ruguje.

Ma’aikatan jinya sun ce suna kula da mutane fiye da 40 da aka ceto daga ɓaraguzan gidajen su da suka rushe.

Ƙaramin yanki ne girgizar ƙasar ta faru, kuma ana ci gaba da samun bayanai kan yawan mutanen da suka mutu da kuma aikin ceto.

KU KUMA KARANTA: Girgizar ƙasa mai karfin gaske ta kashe mutane 296 a Maroko

An samu ƙarin girgizar ƙasa uku da suka faru a yankin jim kaɗan bayan wannan, inda mutane suka ƙauracewa gidajen su don tsoron abin da zai iya faruwa.

Daga cikin yankunan da aka jiyo girgizar ƙasar dai harda birnin Delhi na ƙasar India.

Nepal ta yi fama da mummunar girgizar ƙasa a shekarar 2015, inda mutane aƙalla dubu tara suka mutu, wasu da dama kuma suka samu rauni.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...