No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tsohon kakakin majalisar wakilan Najeriya Femi Gbajabiamila ya sauka daga kujerarsa ta ɗan majalisar wakilan Najeriya, domin fara aiki a sabon muƙaminsa na shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa.

Sabon kakakin majalisar Tajudeen Abbas ne ya karanto wasiƙar murabus ɗin nasa a zauren majalisar ranar Laraba.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ne ya naɗa Gbajabiamila a matsayin sabon shugaban ma’aikata na fadarsa.

Femi dai ya samu nasara a zaɓen kujerar ɗan majalisar wakilan ƙasar mai wakiltar mazaɓar Surulere ta ɗaya a jihar Legas.

KU KUMA KARANTA: Mambobin ASUU su kwantar da hankalin su kan batun albashi – Gbajabiamila

An dai yi ta nuna damuwa kan yadda ɗan majalisar zai tafiyar da muƙaman biyu, bayan da ya ƙarbi rantsuwa tare da sauran ‘yan majalisar sabuwar majalisa ta 10 ranar Talata, har ma ya jefa ƙuri’arsa a zaɓen shugabannin majalisar.

A yanzu hukumar zaɓen ƙasar za ta shirya zaɓen cike-giɓi na ɗan majalisar wakilan mazaɓarsa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...