No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shirin Samar da Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya wato World Food Programme (WFP) ya yi gargaɗi cewa akwai yiwuwar Gaza ya yi fama da matsanancin ƙarancin abinci, yana mai jaddada cewa abincin da ake kai wa bai isa ba wurin magance matasalar yunwa a yankin.

“Akwai matukar yiwuwar mutanen Gaza, musamman mata da ƙananan yara, za su fuskanci matukar ƙarancin abinci idan Shirin WFP bai ci gaba da samar da abinci ba,” in ji wata sanarwa da Shirin na WFP ya fitar.

KU KUMA KARANTA: An kashe Falasɗinawa 100 a hare-haren da aka kai musu cikin dare a Gaza

” WFP na matukar buƙatar abincin da zai bai wa fiye da mutum 120,000 a Gaza a matakin farko,” a cewar sanarwar.

Samer Abdeljaber, wakilin WFP kuma darakta a yankin Falasɗinu, ya ce tawagarsa ta ga yadda mutane suke cikin “yunwa da bala’i da rushewar muhallansu” kuma ba su samu agaji ko ɗaya ba cikin makonnin da suka gabata.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...