No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tsarin lafiya na Gaza ya kusa durƙushewa kuma yankin ba zai kai labari ba idan aka sake rasa motar ɗaukar marasa lafiya ko gadon asibiti, kamar yadda Hukumar Lafiya ta Duniya ta yi gargaɗi.

Kakakin hukumar ta WHO Christian Lindmeier ya shaida wa taron manema labarai a Geneva cewa, “Al’amarin yana ƙara ta’azzara a kowace rana… fiye da zato.”

“Tsarin kiwon lafiya ya durkushe. Gaza ba za ta iya yin asarar wasu cibiyoyin kiwon lafiya ba, ko wata motar ɗaukar marasa lafiya guda ɗaya, ko wasu asibitoci… ko ma gadon asibiti guda ɗaya.”

KU KUMA KARANTA: Harin bam na Isra’ila ya kashe mutane da dama ya jikkata wasu a Birnin Gaza

Lindmeier ya ce yara da mutane suna “bara kuma suna kukan neman ruwa.”

“Muna kan wannan matakin, inda ba a samun kayayyakin yau da kullum da na yau da kullun,” in ji shi. “A yanzu ruwan da ake samu Gaza bai wuce lita ɗaya zuwa biyu ba a rana – wato ruwa rayuwa ne, ba kawai na sha ba. Wayewa ci gaba suna gab da wargajewa.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...