Connect with us

Labarai

Gaskiyar abin da ya faru game da matar da ta kashe mijinta a Bauchi.

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Hukumar ‘yan sanda a jihar Bauchi ta tabbatar da labarin kisan da maimunatu ta yi kisan gilla ga mijinta mai suna Aliyu Mohammad.

Maimunatu Sulaiman ‘yar shekara 21 a duniya da ke zaune a unguwar ƙofar Dumi a ƙwaryar Bauchi ta kashe mijinta, Aliyu Mohammad sakamakon rashin jituwar da ta ɓarke a tsakaninsu.

Majiya daga yankin ta bayyana cewa an samu rashin jituwa ne a tsakanin miji da matar, sakamakon yunƙurin da mijin ya yi na ƙara aure.

A wani ruwayar kuma ance mijin nata yana mata faɗa ne kan fita yawo da take yi.

Bayan samun husuma cikin dare tsakanin su matar ta ɗauki wuƙa ta daddaɓa wa mijin wuƙa ne a ƙirjinsa da gefen cikin sa wajajen da ake ƙira da makasa wanda hakan ya yi sanadin ajalinsa.

Hakan ya faru ne a ranar 5 ga watan Yulin 2023 a unguwar Ƙofar Dumi. Yanda wasu suka sheda mana cewa wuƙar ma ta karɓi aron tane!

KU KUMA KARANTA: An tsinci jariri da ransa, bayan sa’o’i 24 da kashe mahaifiyarsa

Yanzu haka dai rundunar ‘yan sandan jihar, ta ce sun cafke matar da ake zargi da kisan kan.

A sanarwa da kakakin ‘yan sandan jihar, Bauchi ASP Aminu Gimba Ahmed ya fitar a ranar Juma’a ta ce, “A ranar 5 ga watan Yuli 2023 jami’an caji ofis ɗin ‘yan sanda da ke Township, Bauchi sun kama wata Maimunatu Sulaiman kan zargin aikata kisan kai.

“Lokacin da jami’an suka samu rahoton faruwar lamarin, sun garzaya zuwa inda lamarin ya faru tare da ɗaukar wanda lamarin ya rutsa da shi da ita kanta wadda ake zargi zuwa asibitin koyarwa na Abubakar Tafawa Ɓalewa da ke Bauchi.

“Amma likitoci sun tabbatar da mutuwar mijin sakamakon rauni da ya samu a ƙirjinsa, yayin da ita kuma wadda ake zargin ta samu wasu raunuka a cikinta.” da ake zargin ta yanka kanta ne domin ɓat da sawu da za’a iya zaton hari aka kai musu su duka.

Binciken ‘yan sanda ya nuna cewa wadda ake zargin ta soki mijinta a ƙirjinsa sakamakon rashin jituwar da ta ɓarke a tsakaninsu.

Wadda ake zargin ta amsa laifin da ake tuhumarta da shi.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Auwal Musa Mohammad, ya umarci mayar da binciken lamarin zuwa sashen kula da manyan laifuka (SCID) don zurfafa bincike.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like