No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Najeriya ƙarƙashin mai horar da ƙungiyar Jose Peseiro za ta nemi kare maratabar ta da kuma neman ganin ta tsallaka mataki na gaba a wanan gangami,yayin da a ɗaya ɓangaren, Kamaru a cewar mai horar da ita, Rigobert Song za su kasance a kan bakar su na ganin sun doke Najeriya.

A tarihi, haɗuwar waɗannan ƙungiyoyi Najeriya da Kamaru a shekarun baya suka kasance gagara badau a fagen tamola, Najeriya da Kamaru sun haɗu sau 22. Najeriya ta samu nasara a wasanni 11 da ta buga da Kamaru. Yayin da Kamaru ta samu galaba a kan Najeriya sau huɗu ƙungiyoyin biyu sun yi canjaras sau bakwai.

A tarihin lashe kofin gasar Afirka na ƙwallon ƙafa baya ga Masar, da ta lashe Kofin sau 7, Kamaru ta ɗaga wannan kofi sau 5 sai Ghana sau 4.

A ɓangaren Najeriya, ƙungiyar Super Eagles ta lashe kofin sau uku, a shekarar 1980,1994 sai 2013.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...