Connect with us

Labarai

Ganduje ya sayar da ginin hukumar kula da harkokin gwamnatin Kano a ɗansa

Published

on

Kwamitin miƙa mulki na NNPP ya bankaɗo Kwamitin karɓo kadarorin gwamnati na jam’iyyar ‘New Nigeria People’s Party’ (NNPP), ya bankaɗo yadda Gwamna Abdullahi Ganduje ya sayar wa ɗansa Abba Ganduje ginin ofishin hukumar kula da harkokin gwamnati ta jihar Kano.

Shugaban kwamitin, Abdullahi Baffa-Bichi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ziyarar da ya kai hukumar, wacce aka fi sani da ‘Due Process Office’.

A wata sanarwa da Sanusi Dawakin-Tofa, kakakin zaɓaɓɓen gwamnan Kano ya fitar a ranar Alhamis, ya ce ginin kamar yadda kwamitin ya gano an sayar da shi ne ga ɗan Ganduje kan kuɗi Naira miliyan 10.

A cewar Baffa-Bichi, ginin da darajarsa ta kai Naira miliyan 500, an yi zargin cewa ɗan gwamnan ya siyar da shi ne a kan Naira miliyan 300 bayan ya saye shi a kan ƙasa da Naira miliyan 10, kuma za a rusa shi a ranar Alhamis.

KU KUMA KARANTA: Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano zai sake duba batun tsige Sanusi – Kwankwaso

Ya ce wannan matakin “kamar ɓarna ne’ na kowane tsarin mulki kuma wannan ba shi ne abin da ake tsammanin gwamnatin da ta samu damar mulkin jihar na tsawon shekaru takwas ba”.

“Mun damu matuƙa, yadda gwamnatin mai barin gado ke yin jinginar hannun jarin jama’ar kirki na jihar Kano ya bar abin da ake so.” “Wannan wuri (Due Process Office) an sayar da shi ne a kan ƙasa da Naira miliyan 10 kuma muna sane da cewa yaron ya sayar da shi sama da Naira miliyan 300.

“Gaskiya kuna ba shi wurin kyauta kuma kuna neman ya je ya sami mai siya. “Muna jin cewa wannan shi ne mafi girman ɓarnar dukiyar jama’a da kowa zai yi tunaninsa.

“Abin da suke yi, in ji shi, wasan kwaikwayo ne kawai. Sanarwar ta ƙara da cewa za a fara wasan ne daga ranar 29 ga watan Mayu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa gwamnatin jihar Kano mai jiran gado ta Abba Yusuf ta ce za ta binciki duk wata hanya ta doka don ƙwato dukiyoyin al’umma da ake zargin Gwamna Ganduje ya siyar wa iyalansa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like