No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta ce wasu fusatattun matasa sun kashe mutum ɗaya tare da ƙona gidaje 64 da babura 3 da kuma lalata dukiyoyi na miliyoyin Nairori a ƙaramar hukumar Ɓagoro da ke jihar.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Ahmed Wakil, ya rabawa manema labarai ranar Lahadi a Bauchi.

Ya ce hakan ya faru ne a sakamakon zanga-zangar da wasu fusatattun matasa suka yi na nuna rashin amincewarsu da naɗin sarautar Hakimin ƙauyen Sang a ƙaramar hukumar.

KU KUMA KARANTA: An yankewa mahaifiya hukuncin ɗaurin rai da rai, bisa laifin kashe ‘yarta

“A ranar Asabar 15 ga Afrilu, 2023 da misalin ƙarfe 7:00 na yamma rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta samu ƙiran wayar tarho kan wani rikici da ya ɓarke a yankin Ɓagoro na jihar.

“Bincike na farko ya nuna cewa rikicin ƙabilanci a ƙauyen Sang na ƙaramar hukumar Ɓagoro ya samo asali ne daga naɗin sarautar Hakimin Sang.

“Wasu fusatattun matasa masu ayyuka daban-daban sun yi zanga-zangar nuna adawa da naɗin sarautar sun kai hari kan ‘yan ƙasa da ba su ji ba ba su gani ba, yayin da matasan da suka fusata suka ƙona gidaje 64, babura 3 da kuma kadarori na miliyoyin Naira,” in ji Mista Wakil, babban sufeton ‘yan sanda.

Ya ƙara da cewa mutum ɗaya mai suna Apollo Ɗanlami mai shekaru 70 ya mutu a lamarin yayin da wata Naemiya Bature mai shekaru 65 da kuma wasu mutane suka samu raunuka sakamakon wannan ta’asa.

Kakakin ya ce jami’an ‘yan sandan da suka haɗa da tawagogin dabara, da tawagar ɗaukar matakai cikin gaggawa da kuma aikin maido da zaman lafiya cikin gaggawa suka amsa ƙiran da aka yi musu da kuma ƙoƙarinsu na shawo kan lamarin.

“Yankin yana da kwanciyar hankali a yanzu, kuma an ƙarfafa matakan tsaro a cikin ƙaramar hukumar Ɓagoro da kewaye saboda kare lafiyar ‘yan ƙasa ya kasance babban fifikon hukumar yayin da ake aiki dare da rana don ci gaba da lalacewa,” Mista Wakil yace.

A cewarsa, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Aminu Alhassan, ya umurci DPO na Ɓagoro da ya fara gudanar da bincike na gaskiya domin bankaɗo al’amuran da suka haifar da wannan rikici.

Ya bayyana cewa an ƙara ƙaimi wajen ganin an kamo waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki domin fuskantar fushin doka.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...