No menu items!

Sample Page Title

Date:

Fursunoni 281 sun tsere a Maiduguri sakamakon ambaliyar ruwa – NCS

Hukumar da ke Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Najeriya (NCS), ta ce fursunoni 281 ne, suka tsere sakamakon ambaliyar ruwa da ta shafe wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

Kakakin hukumar, Umar Abubakar, ya ce: “Wannan lamari mara daɗi ya haifar da ɓarna, inda ya rushe katangarar gidajen gyaran hali da suka haɗa da matsakaicin cibiyar tsaron hukumar ta Maiduguri (MSCC).”

Ya bayyana cewa: “Bayan kwashe fursunonin da jami’an hukumar tare da tallafi daga jami’an tsaro zuwa wani waje mai tsaro, sai aka gano fursunoni 281 sun ɓace.”

KU KUMA KARANTA: Mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri na fuskantar matsalar lafiya – NRC

Ya ƙara da cewa hukumar tana da bayanan fursunonin da suka tsere

Ya ce: “Hukumar tana aiki tare da sauran jami’an tsaro saboda an fara aikin a ɓoye domin ƙara kama su.

“A yanzu haka, an sake kama fursunoni bakwai tare da mayar da su gidan yari, yayin da ake ƙoƙarin gano sauran don a dawo da su.

“Yayin da ake wannan ƙoƙarin, akwai tabbacin cewa lamarin ba zai kawo cikas ba ko kuma ya shafi lafiyar jama’a ba.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...