No menu items!

Sample Page Title

Date:

Fursunoni 16 sun tsere daga Kurkukun Keffin jihar Nasarawa

Daga Shafaatu Dauda Kano

Hukumar kula da gidajen yari ta Najeriya (NCS) ta ce fursunoni 16 ne suka tsere daga gidan yari na Medium Security da ke Keffi, jihar Nasarawa, da safiyar ranar Talata.

Mai magana da yawun hukumar, Abubakar Umar, ya ce wasu fursunoni sun karya tsaron wurin, suka kai wa jami’an da ke bakin aiki hari, lamarin da ya haifar da tserewar su.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kai hari kurkukun Kuje

A kokarin shawo kan matsalar, jami’ai biyar sun ji raunuka daban-daban, inda biyu daga cikinsu ke cikin mawuyacin hali suna karbar kulawar gaggawa kamar yadda wata majiya ta tattaro.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...