No menu items!

Sample Page Title

Date:

FRSC ta buƙaci a kawo rahoton tuƙin ganganci a kan tituna

A ranar Juma’a, hukumar kare aukuwar hatsurra ta Najeriya (FRSC) ta buƙaci matafiya su kai rahoton tuƙin ganganci akan tituna domin rage yawaitar afkuwar hatsura a watannin karshen shekarar bana.

FRSC ta yi wannan kira ne bayan da ta kammala gangaminta na wayar da kan al’umma a kan watannin karshen shekara.

Taken gangamin na bana shine “yi magana a kan tukin ganganci: hatsura sun fi hallaka fasinjoji fiye da direbobi”.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Afrika na ci gaba da aika wa Trump saƙon taya murna

A ranar 6 ga watan Nuwambar da muke ciki, reshen jihar Filato na hukumar ta FRSC ya kaddamar da nasa gangamin wayar da kan al’ummar a birnin Jos.

A jawabinsa yayin bikin kaddamar da gangamin, Kwamandan FRSC na jihar, Maxwell Plateau, ya jaddada bukatar samun sauyin dabi’a a tsakanin direbobi.

Ya jaddada cewa fasinjoji na da hakkin a tukasu cikin aminci tare da karfafa musu gwiwar jan kunnen direbobin da suka karya dokokin tuki.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...