No menu items!

Sample Page Title

Date:

Femi Falana, SAN, ya bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin makonni biyu da ta biya diyya ga waɗanda harin da sojoji suka kai musu a cikin shekaru bakwai da suka gabata ya rutsa da su, ko kuma ta gurfanar da FG a gaban Kotu.

Lauyan kare hakkin ɗan Adam ya yi wannan gargaɗin ne a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, 10 ga watan Disamba.

Ya ce za a gurfanar da gwamnati a gaban wata babbar kotun tarayya idan har ba a ci wa buƙatar ba.

Fararen hula da dama ne suka mutu a tsawon shekaru sakamakon tashin bama-bamai na bazata da sojojin Najeriya suka kai kan al’umma 

“Gwamnatin tarayya ta biya isassun diyya ga waɗanda harin ya rutsa da su ta sama a Najeriya cikin shekaru bakwai da suka gabata. Idan ba a biya mu bukatarmu nan da makonni biyu masu zuwa ba, za mu maka gwamnatin tarayya a gaban babbar kotun tarayya domin ta kwato hakkin waɗanda abin ya shafa na rayuwa.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...