Femi Falana ya bai wa FG wa’adin mako biyu don biyan diyya ga waɗanda harin jirgin da sojoji suka kai musu bisa kuskure

0
125

Femi Falana, SAN, ya bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin makonni biyu da ta biya diyya ga waɗanda harin da sojoji suka kai musu a cikin shekaru bakwai da suka gabata ya rutsa da su, ko kuma ta gurfanar da FG a gaban Kotu.

Lauyan kare hakkin ɗan Adam ya yi wannan gargaɗin ne a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, 10 ga watan Disamba.

Ya ce za a gurfanar da gwamnati a gaban wata babbar kotun tarayya idan har ba a ci wa buƙatar ba.

Fararen hula da dama ne suka mutu a tsawon shekaru sakamakon tashin bama-bamai na bazata da sojojin Najeriya suka kai kan al’umma 

“Gwamnatin tarayya ta biya isassun diyya ga waɗanda harin ya rutsa da su ta sama a Najeriya cikin shekaru bakwai da suka gabata. Idan ba a biya mu bukatarmu nan da makonni biyu masu zuwa ba, za mu maka gwamnatin tarayya a gaban babbar kotun tarayya domin ta kwato hakkin waɗanda abin ya shafa na rayuwa.”

Leave a Reply