Labarai
El-Rufai ya sake ganawa da jiga-jigan jam’iyyar SDP a Abuja
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/el-rufai-6-768x576-1.jpg)
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna ya sake ganawa da waɗansu jiga-jigan jam’iyyar SDP a gidan Sanata Abubakar Gada tare da shugaban jam’iyyar na kasa Shehu Musa Gabam.
Wannan zama dai shi ne kusan na uku a kasa da kwana goma tun da El-Rufai ya fara bayyana a wani taro mai kama da siyasa.
Ziyarar ta El-Rufai ta fara yamutsa hazo a fagen siyasa wadda wasu ke ganin tana nuna ina ya dosa a zaɓen 2027 da ke tafe ne.
El-Rufai ɗaya ne daga cikin waɗanda suka tsaya kai da fata sai Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya mulki ƙasar nan.
KU KUMA KARANTA: Ministan Harkokin Wajen Turkiyya ya gana da Haniyeh, jagoran siyasa na Hamas, kan tsagaita wuta a Gaza
Sai dai wani abin mamaki El-Rufain bai samu sahalewar Majalisar Dattawan Najeriya domin zama minista a gwamnatin da ya ba da gagarumar gudunmawa wurin kafawa ba.
Yayin wannan taro, an ga Sanata Teslim Folarin, na jam’iyyar APC daga Jihar Oyo, da Sanata Nazif Suleiman, wani jigo a jam’iyyar PDP daga Jihar Bauchi.
A makon da ya gabata dai El-Rufai ya shirya wani shan ruwa inda aka ga mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Malam Nuhu Ribadu da Kashim Ibrahim-Imam (wani jigo a jam’iyyar APC), Shehu Musa Gabam shugaban jam’iyyar SPD na ƙasa, da waɗansu manyan ’yan siyasa.
Mai taimakawa Malam Nasiru a bangaren kafafen sadarwa Muyiwa Adekeye ya ce wannan taro ne kawai na sada zumunta wanda kowa na iya shiryawa.
Ya ce “tsabagen siyasar da ke zuciyar mutane ne ya sa ake yi wa ziyarce-ziyarcen fassarar siyasa, amma wannan ba wani abu ba ne, zumunci ne kawai.”
Muyiwa Adekeye ya yi wannan martani ne ga waɗanda ke cewa El-Rufai na shirin tsayawa takara ne a karkashin jam’iyyar SPD a zaɓen 2027.
Waɗansu hotunan ganawar El-Rufai da jiga-jigan jam’iyyar SDP
'Yansanda
An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci
![An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/2c27c23e2a85f90c.jpg)
An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci
Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.
Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.
A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.
Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.
KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe
Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.
Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.
Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.
Labarai
Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma
![Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/c04cfafecee80694.jpg)
Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma
A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.
Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.
Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.
A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.
KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano
Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.
Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.
Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.
Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.
Labarai
’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe
![’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/thumbs_b_c_2be0ec1ee34177737ad8fde548ea1f3d.jpg)
’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe
Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin
Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.
Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.
Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.
Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.
Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.
Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.
KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara
“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.
“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.
“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.
Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.
“Don haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano