No menu items!

Sample Page Title

Date:

EFCC ta gayyaci shugaban NAHCON, Farfesa Saleh Pakistan kan zargin ɓatan Naira biliyan 50

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta kaddamar da bincike a kan Farfesa Saleh Abdullahi Usman, Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON), kan wasu makudan kudade da suka shafi ayyukan Hajji na 2025.

A cewar majiyoyi, Usman ya gabatar da kansa a hedikwatar EFCC da safiyar ranar Laraba, don amsa gayyatar da aka yi masa.

KU KUMA KARANTA: Shugaba Tinubu ya umurci NAHCON ta rage kuɗin Hajjin bana

Daga baya an sake shi bisa beli amma ana buƙatar ya kai kansa Hukumar a kullum yayin da ake ci gaba da bincike.

Binciken ya biyo bayan zarge-zargen cin hanci da rashawa da ake ta tafkawa a cikin Hukumar, da suka haɗa da karkatar da wasu maƙudan kuɗaɗe da suka kai sama da Naira biliyan 50.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...