No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta naɗa kwamiti na shugabanni uku da zai tattauna da sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar kan mayar da mulki hannun farar-hula sannan ya duba yiwuwar janye takunkuman da aka kakaɓa wa ƙasar.

Shugabannin ƙungiyar ta ECOWAS sun bayyana haka ne a sanarwar da suka fitar bayan taronsu na shekara-shekara a Abuja ranar Lahadi.

ECOWAS ta naɗa kwamitin shugabannin ƙasashen Togo, Saliyo da Benin domin tattaunawa da sojojin Nijar don su amince “da jadawalin miƙa mulki a ɗan ƙanƙanin lokaci” sannan su “gaggauta dawo da tsarin mulki”.

KU KUMA KARANTA: Sojoji sun roƙi kotun ECOWAS ta tilasta wa makwabtan Nijar ɗage takunkumai

Shugaban Saliyo Julius Maada Bio, da shugaban Benin Patrice Talon da kuma shugaban ƙasar Togo Faure Gnassingbe za su gana da sojojin na Nijar domin ganin “sun bar mulki a ƙanƙanin lokaci”, a cewar ƙungiyar.

ECOWAS ta ce: “Za a rika janye tankunkuman da aka sanya wa Nijar ne daki-daki bisa la’akari da sakamakon tattaunawar da kwamitin shugabannin ƙasashen ya yi da sojojin na Nijar”.

ECOWAS ta ce idan sojojin Nijar suka gaza bin ƙa’idojin da shugabannin ƙasashen uku da ke kwamitin suka ba su, ba za a cire wa ƙasar takunkumai ba kuma za a duba yiwuwar amfani da karfin soji.

Kazalika ƙungiyar ta jaddada ƙiran da ta yi wa sojojin Nijar na sakin Mohamed Bazoum da dukkan mutanen da suka kama ba tare da wani sharaɗi ba.

Tun da farko, shugaban Nijeriya Bola Tinubu, wanda kuma shi ne shugaban ECOWAS, ya ce ƙungiyarsu za ta yi ƙoƙarin tattaunawa da ƙasashen da ke ƙarƙashin mulkin soji domin mayar da mulki hannun farar-hula “a lokaci ƙanƙani”.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...