Connect with us

Ƙasashen Waje

ECOWAS ta damu kan ɗaga zaɓen shugaban ƙasa a Senegal

Published

on

Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta nuna matuƙar damuwarta game da matakin da shugaban Senegal ta ɗauka na ɗaga babban zaɓen ƙasar.

Ranar Asabar Shugaba Macky Sall ya sanar da ɗage zaɓen ƙasar wanda aka tsara gudanarwa a ranar 25 ga watan Fabrairun 2024.

Ya sanar da hakan a wani jawabi da ya yi wa ƙasar a Dakar babban birnin ƙasar inda ya ce an ɗage zaɓen sakamakon wasu matsaloli da ke tattare da jerin sunayen ƴan takara.

A Nuwambar bara ne Mista Sall ya saka ranar 25 ga watan Fabrairu a matsayin ranar zaɓen ƙasar inda ƴan takara 20 za su fafata a zaɓen sai dai a cikin mutanen babu sunayen wasu manyan ƴan adawa.

Sai dai a jawabin da Sall ya yi a ranar Lahadi, ya ce ya saka hannu kan wata doka wadda ta yi watsi da hanyar da aka bi wurin saka ranar a baya inda ya ce ƴan majalisa za su gudanar da bincike kan wasu alƙalai biyu dangane da martabarsu sakamakon suna da alamar tambaya a tattare da su ta fuskar zaɓe.

KU KUMA KARANTA: Yau ce ranar zaɓen cike gurbi da raba gardama a jihohi 26 na Najeriya

Sall ya sha nanata cewa zai miƙa mulki a watan Afrilu zuwa ga wanda ya ci zaɓe.

Bayan sanar da cewa ba zai yi takara ba a karo na uku, Sall ya bayyana Firaiminista Amadou Ba wanda ɗan jam’iyyarsa ne a matsayin magajinsa.

Kotun ƙasar ta cire sunayen gomman ƴan takara da zaɓen daga ciki har da ɗan adawar nan Ousmane Sonko da Karim Wade, ɗan gidan tsohon shugaban ƙasar Abdoulaye Wade.

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ranar Asabar da maraice, ta bayyana “damuwa game da yanayin da ya sa aka ɗage zaɓukan” sannan ta yi ƙira ga “hukumomin da suka kamata su yi gaggawar kammala tsare-tsare domin a sanya sabuwar ranar zaɓe.”

Kazalika ECOWAS ta yi ƙira ga dukkan ‘yan siyasar Senegal su mayar da hankali wurin yin sulhu a tsakaninsu tare da haɗa kai wajen ganin an gudanar da sahihin zaɓe.

Haka kuma ƙungiyar ta jinjina wa Shugaba Salla bisa cika alƙawarin da ya ɗauka na ƙin sake tsayawa takara a zaɓen da ke tafe.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like