No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnan jihar Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje, a ranar Litinin ya miƙa ragamar mulkin jihar ga magajinsa, Abba Yusuf, da suka haɗa da basussukan Naira biliyan 241.

Taron ya gudana ne a gidan gwamnati dake Kano.

Ganduje ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar Usman Alhaji, inda ya ce Ganduje ya tafi Abuja ne domin halartar bikin rantsar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasa, Bola Tinubu.

A cewar Ganduje, gwamnatinsa ta tara Naira tiriliyan 1.2 a cikin shekaru takwas da suka wuce, inda ta kashe kuɗaɗen, inda ta bar basussuka kusan Naira biliyan 241.

Ya bayyana cewa basussukan sun haɗa da lamuni, wajibcin kwangila da sauran basussuka.

Da yake karɓar takardun miƙa takardun miƙa mulki, zaɓaɓɓen gwamnan ya nuna rashin jin daɗinsa kan yadda ake bin gwamnati mai jiran gado.

KU KUMA KARANTA: Ganduje ya miƙa mulki ga Abba Yusuf ranar lahadi saboda zai halarci bikin rantsar da Tinubu

“Za mu yi nazarin rahotannin a tsanake sannan mu fito da matsayinmu kan bashin da sauran batutuwa.

“Na yi mamakin yadda gwamna mai barin gado ba ya kusa ya damƙa mani a matsayina na zaɓaɓɓen gwamna, wanda ya kasance al’ada.

“Duk da haka, za mu yi nazarin rahotannin a hankali kuma mu fito da matsayinmu,” in ji Abba Yusuf.

Ya yi ƙira ga al’ummar jihar da su yi wa gwamnatinsa addu’a domin samun nasara tare da tabbatar da ta cimma burin da ake sa ran ta hanyar gudanar da mulkin dimokaraɗiyya.

Waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Kawu Sumaila; da tsohon mataimakin gwamna Hafiz, Abubakar; shugaban ma’aikatan jihar Usman Bala; da shugaban NNPP na jiha Umar Doguwa da sauran manyan baƙi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...