Connect with us

Labarai

Duk da cewa Ganduje ya karɓi naira tiriliyan 1.2 a cikin shekaru 8, ya bar bashin biliyan 241

Published

on

Gwamnan jihar Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje, a ranar Litinin ya miƙa ragamar mulkin jihar ga magajinsa, Abba Yusuf, da suka haɗa da basussukan Naira biliyan 241.

Taron ya gudana ne a gidan gwamnati dake Kano.

Ganduje ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar Usman Alhaji, inda ya ce Ganduje ya tafi Abuja ne domin halartar bikin rantsar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasa, Bola Tinubu.

A cewar Ganduje, gwamnatinsa ta tara Naira tiriliyan 1.2 a cikin shekaru takwas da suka wuce, inda ta kashe kuɗaɗen, inda ta bar basussuka kusan Naira biliyan 241.

Ya bayyana cewa basussukan sun haɗa da lamuni, wajibcin kwangila da sauran basussuka.

Da yake karɓar takardun miƙa takardun miƙa mulki, zaɓaɓɓen gwamnan ya nuna rashin jin daɗinsa kan yadda ake bin gwamnati mai jiran gado.

KU KUMA KARANTA: Ganduje ya miƙa mulki ga Abba Yusuf ranar lahadi saboda zai halarci bikin rantsar da Tinubu

“Za mu yi nazarin rahotannin a tsanake sannan mu fito da matsayinmu kan bashin da sauran batutuwa.

“Na yi mamakin yadda gwamna mai barin gado ba ya kusa ya damƙa mani a matsayina na zaɓaɓɓen gwamna, wanda ya kasance al’ada.

“Duk da haka, za mu yi nazarin rahotannin a hankali kuma mu fito da matsayinmu,” in ji Abba Yusuf.

Ya yi ƙira ga al’ummar jihar da su yi wa gwamnatinsa addu’a domin samun nasara tare da tabbatar da ta cimma burin da ake sa ran ta hanyar gudanar da mulkin dimokaraɗiyya.

Waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Kawu Sumaila; da tsohon mataimakin gwamna Hafiz, Abubakar; shugaban ma’aikatan jihar Usman Bala; da shugaban NNPP na jiha Umar Doguwa da sauran manyan baƙi.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: CSO ta nemi EFCC ta kama Ganduje, ta gurfanar da shi kan bidiyon dala | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like