No menu items!

Sample Page Title

Date:

Dole sojojin Najeriya su koyi harsunan gida don samun sahihan bayanan sirri — COAS

Daga Jameel Lawan Yakasai

Babban Hafsan Sojojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya shawarci jami’an Sojojin Najeriya da su ci gaba da koyon yarukan gida da suka samu yayin horo, yana mai cewa wannan muhimmin makami ne wajen tattara bayanan sirri.

Janar Oluyede ya yi wannan kira ne a yau Juma’a a birnin Abuja, yayin bikin kammala horo kan koyon harsunan gida karo na 7/2025 da aka gudanar a cibiyar horar da Sojojin Najeriya (Nigerian Army Resource Centre – NARC).

Babban Hafsan Gudanarwa na Sojojin Ƙasa, Manjo Janar Lawrence Fejokwu me ya wakilci COAS din a wajen taron.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Najeriya sun kashe mataimakin Turji da wasu mayaƙansa da dama

Ya ce: “Dukkan ayyukanmu sun ta’allaka ne da bayanan sirri, kuma ingancin bayanan sirri yana dogara da yadda ake iya sadarwa da al’ummar wuri.”

Ya ƙara da cewa samun kwarewa a harsunan gida zai ƙara yarda tsakanin sojoji da al’umma, ya inganta sadarwa, tare da ƙarfafa ƙoƙarin yaki da kuma dakile barazanar tsaro a ƙasar.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...