No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya jaddada wa Sakataren Waje na Amurka Antony Blinken buƙatar cewa dole ne a dakatar da kisan ƙare dangin da ake yi a Gaza ba tare da ɓata lokaci ba.

Ya jaddada masa hakan ne a wata ganawa da suka yi a birnin Riyadh na Saudiyya a ranar Litinin, inda Fidan ya ce dole a matsa wa Isra’ila lamba don kawo ƙarshen kisan ƙare dangin, ta hanyar tsagaita wuta ta dindindin, da kuma kai kayan agaji Gaza.

Fidan da Blinken sun tattauna a kan abin da ke faruwa a Gaza a baya-bayan nan, kamar yadda majiyoyin diflomasiyya suka ce.

Sun kuma tattauna kan halin da ake ciki a yanzu a Ukraine da kuma dangantakar diflomasiyyar da ke tsakanin Ankara da Washington.

KU KUMA KARANTA: Kwamitin Tuntuɓa kan Gaza, da Turkiyya sun tattauna kan zamowar Falasɗinu ƙasa mai ‘yanci

Fidan da Blinken sun yi ƙwarya-ƙwaryar ganawar ne ta masu ruwa da tsaki a lamarin Gaza, a wani ɓangare na Babban Taron Tattalin Arziki na Duniya, kamar yadda Ministan Harkokin Wajen Turkiyyan ya wallafa a shafin X.

An samar da ƙungiyar masu ruwa da tsaki kan Gaza ta Gaza Contact Group ne a wani taron Ƙungiyar Ƙasashen Musulmai OIC da Ƙungiyar Ƙasashen Larabawa a watan Nuwamba don dakatar da rikicin da ake yi a Gaza da kuma taimakawa wajen cimma zaman lafiya na dindindin.

Isra’ila ta ƙddamar da mummunan yaƙi a kan Falasɗinu tun bayan da ƙungiyar Hamas ta kai mata wani harin ba-zata ranar 7 ga watan Oktoban bara.

An kashe Falasɗinawa kusan 34,500 tun lokacin, waɗanda mafi yawansu mata ne da yara, sannan an jikkata fiye da mutum 77,600, tare da lalata gine-gine da abubuwan more rayuwa, lamarin da ya jawo fama da ƙarancin abubuwan buƙata.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...