Connect with us

Labarai

Damar tserewa daga Najeriya nake jira — Buhari

Published

on

Tsohon shugaban ya ce ya yi abin da zai iya kuma ya bar ’yan Najeriya su yi alkalanci.

Alfijir Labarai ta rawaito tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari ya ce ba don rufe iyakar Najeriya da Jamhuriyar Nijar da aka yi ba, da tuni ya bar Najeriya ya san inda dare ya yi masa.

A hirarsa ta farko tun bayan sauƙarsa daga mulki, Buhari ya shaida wa gidan talabijin na ƙasa (NTA), cewa duk da cewa ba shi ba ne sugaban ƙasa ba, har yanzu mutane ba su bar shi ya huta ba, inda kullum suke zuwa suna takura masa.

Buhari wanda ya miƙa mulki ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu Mulki a ranar 29 ga watan Mayu, ya ce ya yi iya ƙoƙarinsa a cikin a mulkin da ya yi.

Ya ƙara da cewa ’yan ƙasar suna da wuyar sha’ani wanda hakan ya sa shugabantar su ke da wahalar gaske, amma duk da haka, ya yi iya ƙoƙarinsa.

“Allah ya ba ni damar yi wa ƙasata hidima, kuma na yi iya ƙoƙarina. Amma ko abin da na yi ya wadatar, wannan kuma na bar mutane su yi hukunci.

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya dakatar da buɗe jami’o’i 37 da Buhari ya amince da kafa su

“’Yan Najeriya suna da matukar wuyar sha’ani. Mutane sun san abin da ya kamata su aikata, amma sai su ƙi, saboda suna ganin sun fi wanda ke shugabantar su sanin abin da ya dace.

“Sun san hakkokinsu kuma suna ganin su suka fi dacewa da kujerar ba wanda ke kai ba, don haka, suna sanya ido a kan duk abin da kake yi.

“Saboda haka kai kuma kullun ƙoƙarinka shi ne gwagwarmaya ba dare ba rana don ganin ka yi yadda suke so,” in ji shi.

Da aka tambaye shi game da nagartar muƙarraban gwamnatinsa ta shekara takwas, Buhari ya mayar da martani da cewa “wannan matsalarsu ce.”.

Ya ƙara da cewa ya kamata masu sukar gwamnatinsa su yi wa kansu tambaya kan rawar da kowannensu ya taka a wajen yaƙar cin hanci da rashawa.

Buhari ya bayyana cewa ya naɗa mutane kuma ya ba su damar gudanar da ayyukansu a lokacin da ya ba su ayyuka, yana mai jaddada cewa idan da za a sake ba shi dama, ba zai yi wani abu daban ba a tsarin Najeriya a yanzu.

Tsohon shugaban ƙasar ya bayyana cewa ya amince da sauya fasalin takardun naira ne don kare mutuncinsa da kuma tabbatar wa ’yan ƙasa cewa babu ɓarauniyar hanyar da mutum zai bi domin kaiwa ga nasara a zaɓe.

“Ko ’yan Najeriya sun yarda ko ba su yarda ba, mu ƙasa ce da ba ta ci gaba ba. Kuma a irin wannan yanayi, akwai waɗanda ba su damu da yadda suka tara kuɗi ba.

“Har yanzu ina jin cewa hanya ɗaya tilo da zan iya hana waɗannan mutane ita ce kawai in tabbatar da nagartata… Ina ganin a matsayin ƙasa mai tasowa har yanzu muna da sauran aiki a gabanmu.

“Dalilin da ya sa shi ne don nuna wa ’yan Najeriya cewar babu wata ɓarauniyar hanyar da za a bi wajen samun nasarar jagoranci,” in ji shi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like