Connect with us

Labarai

‘Dalilin da muka lakaɗa wa Alkali duka a Gombe’

Published

on

Rundunar ’yan sandan Jihar Gombe ta kama wasu mutum shida ’yan gida ɗaya da ake zargin su da yi wa alkalin wata babbar kotu dukan kawo wuƙa.

Kakakin ’yan sandan jihar, ASP Mahdi Mu’azu Abubakar, ya bayyana cewa ana shigar da ƙarar waɗanda ake zargin ne a gaban kotun alkalin da suka lakada wa duka, kan shari’ar filin gona.

A cewar sanarwar, ɗaya daga cikin waɗanda ake ƙarar ne ya jagoranci ’yan uwansa suka kai wa alkalin da ma’aikatansa duka a lokacin da suka je duba gonar da ake shari’ar a kanta a garin Potuki da ke yankin Degri ba ƙaramar hukumar Balanga.

Yayin zantawa da Aminiya, ɗaya daga cikinsu ya bayyana cewa suna cikin gona suna aiki ne kawai suka ga mutane sama da 30 suna zagaya gonar, kuma ba su san kowa a cikinsu ba, sai ’ya’yan kawunsu biyu da suke shari’ar gonar da su, kuma kotu ba ta faɗa musu cewa za a zo duba gonar ba.

KU KUMA KARANTA: An yi wa Alkali dukan kawo wuka a Gombe

Abubakar Umaru, ya ce ganin mutanen da yawa da waɗannan ’yan uwan nasu da suke rikicin gonar da su, ta sa zuciya ta ɗebe su suka kai musu hari suka ji musu ciwo ba tare da sanin akwai alkali a cikinsu ba.

“Mun saba ganin mutane suna zuwa gonarmu haka suna dubawa daga ƙarshe kawai sai mu ji an sayar, ba yadda muka iya, shi ya sa a wannan karon ba mu bari ba, muka tarwatsa su” in ji shi.

A cewarsa, daga baya ne suka gane akwai alkali a cikin mutanen, wanda hakan ya sa suka yi nadamar abin da suka aikata.

Abubakar, ya roƙi alkalin da sauran da mutanen da su yafe musu kuskuren da suka yi.

“Wannan shari’ar gadar ta muka yi, domin daga rasuwar mahaifinmu ko addu’ar kwana uku ba a yi ba waɗannan ’yan uwa namu suka kawo mana sammaci a kan cewa mun gaji shari’ar da suke yi da mahaifinmu kan gonar gado tun da shi ya rasu,” in ji shi.

Aminiya ta ruwaito cewa a ranar 4 ga watan Nuwamba 2023 ne mutanen suka yi wa alkalin babbar kotu ta da ke garin Gombe dukan kawo wuka.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like