Connect with us

Labarai

Dalilan da ya sa labaran ƙarya ya fi yaɗuwa – Dakta Hassan Gimba, a hirarsa da RFI Hausa

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Fitaccen marubucin nan kuma ɗan jarida, mawallafin jaridar Neptune Prime, Dakta Hassan Gimba ne ya bayyana haka a hirarsa da gidan Rediyon Faransa (RFI).

RFI HAUSA: Me ya sa labaran ƙarya ya fi yaɗuwa, musamman a kafafen yaɗa labarai na zamani?

DAKTA HASSAN GIMBA: Na farko kafafen yaɗa labarai na Afirka, ko dai na gwamnati ne ko kuma gwamnati tana da alaƙa da su. Don haka shi ya sa ba sa faɗin gaskiya a mafi yawan labaran da suke yaɗawa. Sannan wasu ‘yan jaridar ba su san makamar aiki ba (ba su da ƙwarewa a aikin jarida). Sannan akwai jahilci a wajen wasu masu sauraren, sun fi son labaran nishaɗi. Misali, yanzu a ce ga wani Gwamna yana fitsari a tsaye, to sai an fi tururuwar karanta wannan labarin akan idan ka ce ga wani Gwamna ya gina makarantu.

Su kansu waɗanda ake ƙira ‘yan jaridar, wasunsu ba wai sun ƙware bane a aikin jaridar. To yanzu Allah ya kawo mu wani zamani wadda da zarar mutum ya mallaki babbar waya, ya saka data, shikenan ya zama ɗan jarida. To sune waɗannan masu yaɗa labran ƙarya ɗin. Su kuma mutane sun fi son irin waɗannan labaran. Idan mutum ya rubuta labari na gaskiya, sai ka ga bai fi mutane 20 ko 40 ne suka karanta ba. Amma idan labarin ƙarya aka rubuta, sai ka ga mutane sama da dubu goma sun karanta.

KU KUMA KARANTA: Duk wani juyin mulki idan ya samu awa 24, to ya zaunu – Dakta Hassan Gimba a hirarsa da RFI Hausa

RFI HAUSA: Me ya sa ake yawan samun labarin juyin mulki a ƙasashen Afirka, alhali kuma ba gaskiya bane?

DAKTA HASSAN GIMBA: Su mutane suna ganin duk labaran da suke fito wa daga kafafen yaɗa labarai, ƙarye ne. Sannan kuma suna ganin duk labaran da ya fito daga wajen gwamnati ba gaskiya bane. Shi ya sa idan wani ya zo ya faɗi magana, sai a yi cincirindo a kanta, a ɗauka ita ce gaskiya. Ko irin juye-juyen mulki da ake a yi Afirka. Aka ce an yi a Gabon, sannan aka ce an yi a Kamaru, kuma mutane sun yi cincirindo, sun ɗauka gaskiya ne. Wannan kuma yana da alaƙa da halin ƙunci da ƙaƙa-ni-kayi da al’umma suke ciki.

RFI HAUSA: Kamar jama’a suna sha’awar irin waɗannan labaran ne ko kuma masu yaɗa labaran ne suka yi tasiri a kansu?

DAKTA HASSAN GIMBA: Abin da ya sa shi ne, kusan kowa ya zuba ido ya ga me zai faru a waɗannan wurare, saboda idan an yi juyin mulki a ƙasa kaza, saboda wasu dalilai. To saboda irin waɗannan dalilai, ya kamata a yi ƙasa kaza ma. Su kuma masu shafin yanar gizo, yawan masu bibiyar labaransu, waɗanda suke duba labaransu, a nan suke samun kuɗi da suna. To don haka, shi ya sa suke yaɗa irin waɗannan labaran.

RFI HAUSA: To waɗanne hanyoyi za a bi don daƙile irin waɗannan labaran?

DAKTA HASSAN GIMBA: To ka ga yanzu kamar ku RFI, BBC, DW, VOA da wasu kafafen yaɗa labarai na cikin gida suna iya ƙoƙarinsu. Amma waɗancan masu yaɗa labaran ƙaryar sun fi yawa. Sannan akwai wasu ƙungiyoyi, kamar a ce ‘Wole Soyinka Center For Investigating Journalism’ suna ƙoƙarin tallafa wa gidajen jaridu da gidajen Rediyo masu zaman kansu, domin su tsaya suna faɗin gaskiya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like