Connect with us

Labarai

Da wane dalili masu tuƙa Keke Napep suka shiga yajin aiki a Damaturu?

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

A wani yunƙuri na magance cin zarafi da tarar da ta wuce ƙima da hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Yobe (YROTA) ke ci gaba da yi, direbobin babur masu ƙafa uku da aka fi sani da Keke Napep sun fara yajin aikin a ranar Talata 13 ga watan Fabrairu. Ma’aikatan YOROTA suna cin zarafi mai yawa ga masu tuƙa Keke NAPEP, waɗanda kuma suke karɓar tara mai yawa kan ƙananan laifukan da suka shafi ababen hawa.

Mambobin ƙungiyar Keke Napep da suka zanta da manema labarai a Damaturu, sun bayyana takaicinsu kan lamarin. Sun bayyana rashin adalcin da suke fuskanta da kuma tara ta kuɗi mai da ‘yan YOROTA take ɗora masu. A sakamakon wannan yajin aikin, matafiya da suka haɗa da ɗalibai, ma’aikatan gwamnati, ‘yan makaranta, da sauran jama’a, abin ya shafa, inda aka tilasta musu yin tafiya mai nisa a ƙafa don isa wuraren da za su je. Wannan musamman ya shafi waɗanda ke fama a cikin mawuyacin yanayi na tattalin arziƙi na yanzu.

Bugu da ƙari, yajin aikin ya yi illa ga harkokin kasuwanci da makarantu, musamman ga waɗanda ke nesa da gidajen ma’aikatansu ko ɗaliban. Jama’a na ƙira ga gwamnatin jihar da ta shiga tsakani tare da samar da wasu matakai na gaggawa domin rage wahalhalun da matafiya da ‘yan kasuwa ke fuskanta.

Tattalin arziƙin jihar Yobe da ma ƙasa baki ɗaya ya ƙara taɓarɓarewa sakamakon ƙarancin kuɗi da ƙarancin hanyoyin rayuwa. Yana da matuƙar muhimmanci Gwamnatin Jiha ta magance wannan lamarin cikin gaggawa, duba da irin ƙalubalen tattalin arziƙi da al’umma ke fuskanta.

KU KUMA KARANTA: Masu tuƙa Keke Napep a Yobe, sun koka akan takurawar da hukumar YOROTA ke yi musu

Ta hanyar ɗaukar matakin gaggawa don magance matsalolin da masu aikin Keke Napep suka nuna, gwamnati za ta iya taimakawa wajen dawo da tsarin sufuri da kuma rage wahalhalun da jama’a ke fuskanta.

A halin da ake ciki, ƙoƙarin tuntuɓar hukumar ta YOROTA domin jin ra’ayinsu bai yi nasara ba, domin har zuwa lokacin rubuta wannan rahoto ba a amsa ƙiran wayar wakilinmu ba. Wannan ya nuna gaggawar lamarin da kuma buƙatar ɗaukar matakin gaggawa don dawo da tsarin sufuri da kuma rage wahalhalun da jama’a ke fuskanta.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Tinubu na shirin zuba tiriliyan 2 don bunƙasa tattalin arziki

Published

on

Tinubu na shirin zuba tiriliyan 2 don bunƙasa tattalin arziki

Tinubu na shirin zuba tiriliyan 2 don bunƙasa tattalin arziki

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya umarci tawagarsa ta tattalin arzikin ƙasar su shirya wani tsari na zuba naira tiriliyan biyu, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 1.33 don magance matsalolin da ake da su game da samar da abinci da hauhauwar farashi da kuma ƙarfafa muhimman sassa, in ji Ministan Kuɗi a ranar Alhamis.

Shirin, wanda za a aiwatar da shi tare da haɗin gwiwar gwamnatocin jihohi da kamfanoni masu zaman kansu, zai ware naira tiriliyan ɗaya, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 664.45 ga harkokin noma da samar da abinci da kuma bangaren makamashi, sai wata naira biliyan 350 domin kula da lafiya da walwalar jama’a, kamar yadda Olawale Edun ya fadawa manema labarai.

Tun bayan hawansa mulki a watan Mayun bara, Tinubu ya aiwatar da sauye-sauye da suka haɗa da rage tallafin man fetur da wutar lantarki da kuma rage darajar Naira sau biyu, a yayin da yake fafutukar ƙara zuba jari da ƙara yawan kayayyakin da ake samarwa.

KU KUMA KARANTA: Ɗangote ya soki sabon tsarin gwamnatin Tinubu

Sai dai tattalin arzikin ƙasar ba ya samun ci gaba cikin sauri ƙasa da 6% a duk shekara kamar yadda ya yi fata, yayin da sauye-sauyen suka sa tashin farashin kayayyaki ya kai mafi muni a cikin shekara 28, ya kuma ta’azzara yanayin rayuwa.

“Abu na farko da shugaban ya mayar da hankali a kai shi ne samar da abinci” a cewar Edun ranar Laraba bayan da Tinubu ya ƙaddamar da wani gyara na tsarin tafiyar da tattalin arziki.

Edun ya ce “Jajircewa wajen samar da abinci a farashi mai rahusa da kuma samar da shi da yawa shi ne abin da Shugaban Ƙasa ya fi mayar da hankali a wannan lokaci.”

Har ila yau, shirin na son magance matsalar raguwar yawan man da ake haƙowa da nufin ƙara yawansa zuwa ganga miliyan biyu a kowace rana, ta yadda za a samar da ƙarin kuɗaɗen shiga da kuma musayar kuɗaɗen waje ga tattalin arzikin ƙasar.

Najeriya ta dogara ne da man fetur wajen samun fiye da rabin kuɗaɗen shigarta da kuma kusan kashi 90% na kuɗin waje.

Sai dai yawan man da ake hakowa ya ragu a shekarun baya-bayan nan, inda satar man da zagon kasa da kuma ficewar manyan kamfanoni daga wuraren da ake haƙo man saboda matsalar rashin tsaro, inda suke mayar da hankali kan binciken mai a teku.

Edun bai fayyace lokacin aiwatar da shirin bunƙasa tattalin arzikin ba.

Continue Reading

Labarai

A fara duban watan sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi

Published

on

A fara duban watan sabuwar shekarar Musulunci - Sarkin Musulmi

A fara duban watan sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar ya umarci al’umma da su soma duban watan Muharram na Sabuwar Shekarar musulunci ta 1446 Hijiriyya daga ranar Jumu’a 5 ga watan Yuli, 2024.

A madadin Sarkin Musulmi, Wazirin Sakkwato kuma Shugaban Kwamitin Bayar da Shawara kan Harkokin Addini a Masarautar Sarkin Musulmi, Farfesa Sambo Wali Junaid, ne ya fitar da sanarwar.

Farfesa Sambo, ya ce duk wanda ya samu ganin watan ya sanar da Majalisar Sarkin Musulmi ko wani uban kasa ko hakimi domin sanar da al’umma.

KU KUMA KARANTA: Dole mu kare martabar Sarkin Musulmi – Kashim Shettima

Watan Muharram shi ne watan farko a tsarin watanni 12 na Shekarar musulunci.

Idan an ga watan, Asabar 6 ga watan Yuli, 2024, zai kasance ranar farko a shekarar 1446 Hijiriyya.

Continue Reading

Labarai

‘Yan ta’adda sun kashe mutane sama da mutum 7,000 a Yammacin Afirka a bana – Tuggar

Published

on

‘Yan ta’adda sun kashe mutane sama da mutum 7,000 a Yammacin Afirka a bana - Tuggar

‘Yan ta’adda sun kashe mutane sama da mutum 7,000 a Yammacin Afirka a bana – Tuggar

Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar, ya bayyana buƙatar gaggawa wajen haɗa kai don yaƙi da ta’addanci da sauran matsaloli na rashin tsaro a Yammacin Afirka.

A saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Tuggar ya ce daga watan Janairu zuwa watan Mayun 2024, an samu hare-haren ‘yan ta’adda 800 a Yammacin Afirka, musamman a ƙasashen Burkina Faso, Mali da Nijar.

Ya ƙara da cewa sama da mutane 7,000 ne suka mutu sakamakon hare-haren na ta’addanci a yankin.

KU KUMA KARANTA: Bai kamata ƴan ba-ni-na-iya su shigo da matsalolinsu Gabas ta Tsakiya ba – Turkiyya

“Dole ne mu haɗa kai waje guda don magance matsalolin tsaro, kuma mu yi aiki ba gajiyawa domin tabbatar da tsaro, dimokuraɗiyya da cigaban yankinmu,” in ji Tuggar.

Ya ƙara da cewar a yayin taron, sun kuma sake nazari da duba kan Tsarin Dimokuraɗiyya da Shugabanci na ECOWAS, inda ya kuma yaba da ayyukan samar da zaman lafiya da taimakon jinƙai da ake bayarwa a yankin.

Ƙasashen Yammacin Afirka dai suna fama da hare-hare na ƙungiyoyin da ke da alaƙa da ISIS da Boko Haram ko ISWAP.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like