No menu items!

Sample Page Title

Date:

CBN ta sahalewa ‘yan canji sayen dala dubu 25 a mako guda, saboda bukin kirsimeti

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya bada sahalewar wucin gadi ga masu sana’ar canjin kudade, su sayi abinda ya kai dala 25, 000 a mako guda daga kasuwar hannayen jarin kasar, tsarin da aka kaddamar a farkon watan da muke ciki.

Tsarin zai yi aiki ne a tsakanin 19 ga watan Disamban 2024, zuwa 30 ga watan Janairun 2025.

KU KUMA KARANTA:NAHCON za ta haramta amfani da dala a aikin hajji, don rage tsadar kuɗin kujera

Sanarwar mai ɗauke da kwana wata 19 ga watan Disamban 2024, da sa hannun T. G Allu, a madadin mai rikon mukamin daraktan sashen kasuwanci da musayar kudade na CBN, ya bayyana cewa an tsara matakin ne domin biyan bukatar musayar kudaden ketare a lokacin hutu.

Sanarwar ta kara da cewa hada-hadar za ta gudana ne akan mizanin musayar da CBN ya tsayar ta NFEM, kuma za’a bukaci masu sana’ar musayar kudaden su tsaya a kan ribar da bata zarta kaso 1 cikin 100 ba wajen sayar da kudaden musayar ga masu bukata.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...