No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da ajandar shiri a Najeriya na shekarar 2050 da nufin ƙara haɓaka tattalin arziƙin cikin gida da kashi bakwai cikin ɗari da kuma samar da sabbin ayyuka miliyan 165 a faɗin ƙasar nan.

An ƙaddamar da taron ne jim kaɗan kafin a fara taron majalisar zartarwa ta tarayya na wannan mako a zauren majalisar da ke fadar shugaban ƙasa, Abuja.

Hakan na zuwa ne kimanin makonni bakwai bayan da FEC ta amince da daftarin manufofin a ranar 15 ga watan Maris da kusan watanni uku bayan Majalisar Tattalin Arziƙin Ƙasa ta amince da Ajandar.

A nasa jawabin, shugaba Buhari ya tabbatar da cewa, hangen nesan ya samo asali ne daga tsarin tattalin arziƙi mai tsauri na ilimi don samar da ci gaba mai ɗorewa nan da shekarar 2050.

KU KUMA KARANTA: Buhari ya taya ‘yan jarida murnar zagayowar ranar ‘yancin ‘yan jarida ta duniya

Ya kuma bayyana imanin cewa takardar wadda ta yi nufin ƙara kuɗin shiga ga kowane ɗan Najeriya zuwa dala 33,328 a duk shekara.

Za a sanya shi cikin manyan ƙasashe masu ƙarfin tattalin arziƙi a duniya nan da shekarar 2050, za su kasance masu amfani ga gwamnatoci masu zuwa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...