No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya buƙaci majalisar dattawa ta tabbatar da sake naɗa Abike Dabiri-Erewa a matsayin babbar jami’ar hukumar ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje, NIDCOM.

Buƙatar Buhari na ƙunshe ne a cikin wata wasiƙa da ya aike wa shugaban majalisar dattawa, Ahmed Lawan kuma aka karanta a zauren majalisa ranar Talata.

Buhari a cikin wasiƙar ya ce naɗin ya kasance daidai da tanadin sashe na ƙ karamin sashe na 2 na dokar kafa NiDCOM na 2017.

Haka zalika, shugaba Buhari a wata wasiƙa da ya aike wa shugaban majalisar dattawan, ya nemi a tabbatar da sunayen mutane shida da aka naɗa domin naɗa su a matsayin kwamishinonin tattara kuɗaɗen shiga na tarayya da hukumar kula da kasafin kuɗi.

Buhari ya ce buƙatar ta biyo bayan tanadin sashe na 154 ƙaramin sashe na 1 na kundin tsarin mulkin ƙasar na shekarar 1999.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Najeriya ta naɗa Farfesa Mahmud shugaban asibitin ƙasa da ke Abuja

Waɗanda aka zaɓa za su cike guraben da ake da su a wasu jihohi.

Waɗanda aka naɗa sun haɗa da Ayogu Eze (Enugu), Peter Opara (Imo), Hawa Umaru Aliyu (Jigawa). Sauran sun haɗa da Rekiya Haruna (Kebbi), Ismaila Mohammed Agaka (Kwara) da Kolawole Daniel Abimbola (Oyo).

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...