Connect with us

Labarai

Boko Haram na iya shafe Najeriya idan ba a tashi tsaye ba — Zulum

Published

on

Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, ya yi gargaɗin cewa rikicin Boko Haram na iya shafe ƙasar nan idan ba a tashi tsaye don shawo kan shi ba.

Ya yi gargaɗin ne lokacin da yake jawabi bayan ya karɓi baƙuncin kwamitin gudanarwa na Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC) a zauren majalisar dokokin jihar da ke Maiduguri a ranar Litinin.

Ya ce, “Matsayin jihar Borno a taswirar Najeriya yana da matuƙar muhimmanci a gare mu baki ɗaya. Jihar Borno tana da iyaka da Chadi, Kamaru da Jamhuriyar Nijar. Iyakokinmu sun yi yawa don haka tabbatar da tsaro a yankin Arewa maso Gabas ya shafi tabbatar da tsaron ƙasa baki ɗaya.

“Yayin da Arewa maso Yamma da Arewa ta tsakiya da sauran su ke magana kan ’yan fashi, garkuwa da mutane, da sauran su, mu ’yan Boko Haram da ISWAP ne suka addabe mu. Yana da kyau a yi wani abu kafin su mallake jihar.

KU KUMA KARANTA: Babu ƙaramar hukuma ko ɗaya a hanun Boko Haram – Gwamna Zulum

“Dole ne mu dakatar da ɗaukar matasa daga shiga Boko Haram da ISWAP, idan ba haka ba, nan gaba kaɗan, za a shafe duk Najeriya daga taswira,” in ji Gwamna Zulum.

Yayin da yake kokawa kan yawan mutanen da ke gudun hijira, Gwamnan ya ce lamarin na ƙara ta’azzara sakamakon halin matsi da jama’a ke ciki.

“Sannan kuma a Jihar Borno, a 2012, kimanin mutane miliyan 3.5 ne suka rasa matsugunansu. Mun mayar da da yawa amma duk da haka, muna da sama da mutane miliyan ɗaya, mutanen da suka rasa matsugunansu da ke zaune a sansanoni. Wasu na karuwanci, ana shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a sansanonin,” a cewar Zulum.

“Saboda haka muna son hukumar ci gaban Arewa maso Gabas ta shiga tsakani. Muna son ku haɗa kai da gwamnatin jiha domin mu rufe waɗannan sansanonin ‘yan gudun hijira domin mutane su samu abin dogaro da kansu.

“Idan ba haka ba, da yawa daga cikin mutanen za su iya shiga ISWAP da Boko Haram. Waɗannan mutanen da ke zaune a sansanonin ‘yan gudun hijira abu ne mai matuƙar damuwa a gare mu duka. Don haka wannan aiki, na yi wa al’ummar Jihar Borno alƙawarin cewa zan rufe duk wani sansani da ke cikin birnin Maiduguri kuma mun yi hakan da taimakon Allah Maɗaukakin Sarki.

“Yanzu burina na gaba shi ne ganin yadda za mu rufe dukkan sansanonin ‘yan gudun hijira da ke sauran ƙananan hukumomin da babu zaman lafiya.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like