Bayan ya yi kwanaki a hanun masu garkuwa da mutane, an sako babban limamin Ondo

Alhaji Ibrahim Oyinlade, babban limamin unguwar Uso dake ƙaramar hukumar Owo ta jihar Ondo, ya samu ‘yanci daga hannun masu garkuwa da mutane.

Sakin sa na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan masu garkuwa da mutanen sun nemi iyalansa da su biya shi kuɗin fansa naira miliyan 10.

Duk da haka, babu tabbas ko dangin sun biya kuɗin fansa ko kuma malamin ya sami ‘yanci da kansa.

Rahotanni sun bayyana cewa malamin yana aiki ne a gonarsa lokacin da maharan suka mamaye harabar inda suka tafi da shi ranar asabar.

KU KUMA KARANTA : Sai an bamu miliyan 10 za mu sako limamin Ondo – Masu garkuwa da mutane

“Kodayake masu garkuwan sun tuntuɓi ‘yan uwa da safiyar yau (Lahadi) inda suka buƙaci Naira miliyan 10, an sako shi da yammacin yau” in ji wata majiya daga dangin.

Majiyar dangin ba ta bayyana ko an biya kuɗin fansa kafin a sako malamin ba.


Comments

One response to “Bayan ya yi kwanaki a hanun masu garkuwa da mutane, an sako babban limamin Ondo”

  1. […] KU KUMA KARANTA: Bayan ya yi kwanaki a hanun masu garkuwa da mutane, an sako babban limamin Ondo […]

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *