No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Yobe a ranar Asabar ɗin da ta gabata ta ce ta kama wani basarake da ‘ya’yansa biyu kan kisan wani Goni Waje a ƙauyen Dako Kangarwa da ke ƙaramar hukumar Yunusari.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Dungus Abdulkarim ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a Damaturu, ya bayyana sunayen waɗanda ake zargin Jalomi, Ciroma da Bulama.

Mista Dungus, ya ce kisan ya auku ne a ranar 7 ga watan Yuni bayan mutanen uku sun zargi Waje da yin lalata da matar Bulama, hakimin yankin kuma mahaifin Jalomi da Ciroma.

“Kamar yadda shaidun gani da ido suka bayyana, an yi wa mamacin yankan rago tare da kone shi ƙurmus daga hannun Alhaji Jalomi da Ciroma.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe basarake sun ƙona gawarsa a Imo

“Kamar yadda aka ruwaito, lamarin ya fara ne da faɗa da ya kai ga mamacin ya yi amfani da wuƙa wajen raunata mahaifin waɗanda ake zargin,” in ji Mista Abdulkarim.

Ya ƙara da cewa daga baya Bulama ya umurci ‘ya’yansa da su bi Waje, inda suka shi ƙona shi har lahira.

Mista Abdulkarim ya ce waɗanda ake zargin uku sun miƙa kansu ga ofishin ‘yan sanda na yankin Yunusari bayan faruwar lamarin.

“Yayin da Bulama ke neman hanyoyin da zai yi wa kansa magani daga raunin da ya samu, ba shi da wani zaɓi da ya wuce ya sa ‘yan sanda su gudanar da bincike.

“Wanda aka kashe ya bayyana a matsayin wanda ake tuhuma, wanda hakan ya sa aka kama shi a ofishin ‘yan sanda na Yunusari “

Daga baya, waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aikin sun kai rahoton kansu ga sashin Yunusari bayan kama mahaifinsu,” in ji shi.

Mista Abdulkarim ya ce an miƙa mutanen uku zuwa sashin binciken manyan laifuka domin ci gaba da bincike.

Kakakin ya ce an ajiye gawar Mista Waje a asibitin ƙwararru da ke Damaturu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...