No menu items!

Sample Page Title

Date:

Bankin Duniya ya yi hasashen bunƙasar tattalin arziƙin Najeriya a 2025

Bankin duniya ya yi hasashen za a samu matsaikaciyar bunƙasar ta kaso 3.6 a tattalin arziƙin Najeriya a tsakanin shekarun 2025 da 2026 sakamakon sauye-sauyen da gwamnatin tarayyar ƙasar ke gudanarwa.

Bankin ya bayyana hakan ne a cikin rahotonsa, na hasashen tattalin arzikin duniya na bana, da aka wallafa a jiya Alhamis.

Rahoton ya kara da cewa sauye-sauyen baya-bayan nan da gwamnatin Najeriyar ke aiwatarwa sun taimaka wajen bunkasa kwarin gwiwar yin kasuwanci.

KU KUMA KARANTA:Tattalin arzikin Najeriya ya bunƙasa da kaso 3.46 cikin 100 – CBN

Fitattu a cikin sauye-sauyen tattalin arzikin da gwamnatin Najeriyar ke aiwatarwa sune janye tallafin man fetur da kuma kudirorin gyaran dokar harajin da suka janyo cece-kuce.

A cewar bankin duniyar “yawan arzikin da Najeriya ke samarwa, GDP, ya karu da kimanin kaso 3.3 cikin 100 a 2024, inda galibi hada-hadar bangaren ayyuka ne ya samar da shi, musamman bangarorin hada-hadar kudi da harkokin sadarwa.

“Ana hasashen bunkasar arzikin Najeriyar ta kara fadada zuwa kimanin kaso 3.6 cikin 100 tsakanin shekarun 2025 zuwa 2026. Sakamakon manufar takaita hada-hadar kudi ta 2024, ana hasashen raguwar hauhawar farashi sannu a hankali, inda za ta tallafawa bunkasar bangaren ayyuka, wanda ya kasance babban jigo na samun bunkasar arzikin.”

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...