Connect with us

Labarai

Ban ce na fi ƴan Najeriya shan wahalar tsadar rayuwa ba — Ɗangote

Published

on

Attajirin da ya fi kowa kuɗi a Afirka, Alhaji Aliko Ɗangote ya nesanta kansa da wani labari da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta na zamani cewa ya ce ya fi ƴan Najeriya shan wahalar tsadar rayuwa.

Ɗangote ya ce “wasu ne suka ɗauki nauyin yaɗa labarin domin ɓata mini suna, a daidai lokacin da ƴan Najeriya ke cikin halin ƙaƙa-ni-ka-yi saboda wahalhalun da ake fama da su,” kamar yadda sanarwar da kamfaninsa ya fitar ta bayyana.

Shugaban rukunin kamfanonin na Ɗangote ya nemi ƴan ƙasar su yi watsi da labarin, inda ya yi fatan kawo ƙarshen matsalar da ake ciki a Najeriya.

“Duk abin da ya shafi ƴan Nijeriya ya shafe mu”, in ji sanarwar.

KU KUMA KARANTA: Matatar fetur ɗin Ɗangote ta fara samar da dizel da man jirgin sama

Matsalar hauhawar farashi da tsadar rayuwa da matsi na ci gaba da ta’azzara a Najeriya, inda ko a makon da ya wuce wasu al’umma suka yi zanga-zanga a jihar Neja da nufin jawo hankalin gwamnati kan lamarin.

Sai dai gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi suna ta lallashin ƴan ƙasar tare da alƙawarin cewa abubuwa za su yi sauƙi nan ba da jimawa ba.

A sanarwar kamfanin nasa, Ɗangote ya ƙara da cewa, ”an kawo maganar faɗuwar darajar naira da sayen kaya da Dala ne domin cim ma wasu buƙatu na ƙashin kai buƙatun da ba a samu damar biya ba a baya.”

“Mu ma muna sayen muhimman kayan abinci a kasuwa kamar yadda kowa ke saya don amfanin kanmu da kuma bayarwa wajen ciyar da al’umma,” in ji Ɗangote.

Shugaban kamfanin ya kuma bayyana mamaki kan yadda ake neman haddasa saɓani tsakanin Kamfanin Dangote da gwamnatin tarayya, inda ya ce shi ɗan kasuwa ne ba ɗan siyasa ba, don haka babu inda ya yi maganar ƙalubalantar gwamnati.

“Kamfaninmu ya kasance mai bin dokokin ƙasa a ko da yaushe, tare da neman sauƙi ga al’umma da fatan alheri.”

Sanarwar ta nemi ƴan Najeriya su guji ɗaukar saƙon da ba daga kamfanin ya fito ba kai-tsaye, tare da guje wa yaɗa jita-jita.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like