No menu items!

Sample Page Title

Date:

Zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce matansa da ‘ya’yansa ba za su shiga gwamnati ba a harkokin mulkin jihar.

Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabin karɓar takardar shaidar lashe zaɓe. Ya ce, “matana ba za su shiga cikin harkokin mulki ba, haka suma ‘Ya’yana ba za su shiga cikin harkokin mulki ba.

KU KUMA KARANTA: Yadda Abba Kabir Yusuf na NNPP ya lashe zaɓen Kano

“Kuma zan iya gaya muku tabbas haka ne ga mataimakin gwamna na”. In ji shi.

Zaɓaɓɓen gwamnan ya kuma yi kira ga ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC, Nasir Yusuf Gawuna, da sauran ’yan takarar da suka fafata a zaben da aka yi a ranar 18 ga watan Maris, da su shiga gwamnatinsa domin gudanar da ingantaccen shugabanci a jihar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...